Tamkar a mafarki haka Hajjah ta ji wannan albishir na warkewar masoyin ɗanta, murna fal da ranta ta ce "Kai Farouk, da gaske, ko kuma tsokana ta kake?", daga cikin wayar ya shagwaɓe mata " Haba Hajiyata, ta ya zan tsokanar ki, na rantse kuwa ya warke", cike da rikicewar murna ta ce "Ina Deenin?", tana jin lokacin da Lalu ya miƙa ma Deeni wayar, sallamar sa ta ji cikin sanyin murya, bayan ta amsa ne ta ce "Aiki ya yi kyau ko?", ya ce "Eh Hajjah", sai dai bai faɗa mata ba sosai yake gani ba, duk. . .