Malam Yahuza ya ce "Idan Allah ya ga dama zai iya komawa aikinsa mana, tunda lamarin a hannun Allah ya ke, ba a wurinmu ba", kan ka ce me kuwa Bello ya ƙara rikicewa, saboda tunda har idanun Deeni suka buɗe, toh abu ne mai sauƙi a wurin Allah kamar yadda Malam Yahuza ya faɗa, duk da shi Bellon bai cika kai kukansa wurin Allah ba, ya fi tafiya wurin Malamai, waɗanda su ma a wurin Allahn suke nema, toh amma ya san Allah zai iya komai.
"Malam dan girman Allah ka taimaka mani, don muddin. . .