Da farko sallama ce Deena ta yi ma Rahila haɗe da Barka da shan ruwa, daga nan kuma ta ɗora faɗin "Yaya na ta shan addu'aoinku, Allah ya saka da Alkhairi Amiin", tabbas dama Rahila ta san Deena ba zata yi mata wulakanci ba tunda wayayyiya ce, amma kuma bata yi zaton maganar zata zo da taushi haka ba, don ta lura da yadda Deena ke matuƙar kishin mijinta. Ajiyar zuciya Rahila ta sauke kafin ta yi mata reply da "Masha Allah, ai Dr. Ya cancanci addu'ar kowa, Allah ya ƙara masa lafiya", da rawar. . .