Ita ma Munaya hawayen ya ƙwace mata. Cak! Anti Zuwaira ta dakata da kukan da take yi, kamar wacce ta tuna wani abu, ko kuma wacce take cikin halin mamaki. Idanu ta zubawa Munaya, yadda take kuka da iya gaskiyarta, tamkar an yi mata wahayi da mutuwar Umma. Bata kula cewa ita take kallo ba, dan haka ta ci gaba da kukanta, har da zamewa ƙasa tana shure-shure.
"Wayyo Uncle Zayyad, ka tafi ka barmu."Karaf! Ta haɗa idanu da Anti Zuwaira. Hakan yasa ta ɗan shiga taitayinta.
"Dama kin taɓa saninsa ne? A ina kika san. . .