Ta daɗe tsaye a tsakar gidan bayan tafiyarsu. Tunanin Mukhtar zai iya zargin ita ta kira Hajiyarmu ta faɗa mata wannan maganar yasa duk jikinta yayi sanyi. Lokaci ɗaya ta nemi matsanancin farin cikin da ya lulluɓe zuciyarta ta rasa.
Da taga dai tsayuwar bazai mata ba sai ta fara takawa a hankali zuwa cikin falon, hankalinta a tashe, zuciyarta a ɗugunzume.
Ko da tayi sallama bai amsa mata ba, yana zaune a inda suka barshi, har lokacin kanshi a ƙasa.
Saɗaf saɗaf ta kama hanyar shigewa ɗakinta.
"Fareeda"
Ya kira ta da wani irin. . .
Hmm lallai