Ko da suka shiga cikin ɗakin da yake falle ɗaya, sai suka tarar da kujeran zama mazaunin mutum uku ita kaɗai ce a ajiye ta bakin ƙofa.
Can daga cikin ɗakin gado ne, a gefe guda da sauran tarkacen kayayyaki. Kan kujera Baban Murad yayi musu umarnin zama, shi kuma ya ƙarasa gefen gado ya zaunar da Maman Murad. Jikinsa na rawa ya ƙarasa kusa da fanka ƴar tsaye ya kunna ya matsa da fankar kusa da Maman Murad da tayi wata dagwalooo kamar wata wawuya ta ƙura ma guri ɗaya idanu.
Fatima ce ta ɗan ɗofana mazaunanta kan. . .