Mamaki mai tsanani ne ya lulluɓe shi ganin Fatima kwance kan doguwar kujera a falon Hajiyarmu. Ƙam ya tsaya guri ɗaya yana ɗan murza idanunsa, da tunanin ko tsananin caja mishi kai da take yi ne yasa ta fara yi mishi gizo.
Ganin bata ɓace ba yasa shi tabbatar da Fatima ce a gaske.
"Me ya kawo ki gidannan?"
Ya tambayeta cikin tsawa da ɓacin rai.
A kasale ta miƙe ta zauna tana yamutsa fuska. Tunda tayi amannan har yanzu ƙarfin jikinta bai dawo ba. Ta buɗe baki za tayi magana da saurin gaske ya dakatar da. . .
Ciki? Chakwakiya kenan dai
Yanzu kam babu ko wani rabuwa