"Ki rage fita da yarinyar nan saboda bakin mutane da kuma miyagu, idan bikine ko suna ki barta wajen Abu, idan tare zaku je ki biyo ki kawota gida."Shine abinda Innar A'i tace mata lokacin da taje yawon arba'in ta kuma kwance goyon Yelwa tana mika ma Innar A'i da ta karbeta tana kura mata idanuwa. Ko ita haka take saka Yelwa a gaba tana kallo, tana jinjina ma ikon Allah da ya fitar da halitta kyakkyawa kamar Yelwa daga jikinta. Julde na da haske, Yelwa ma haka, amman farin yarinyar wani irin sirki gare shi. . .
Muje zuwa
Tayaya zan samu part 2 na wannan novel din