"Adee..."
Nawfal ya furta bayan sun shigo dakin ita da Khalid suna gaisawa da Daada. Wata irin kewar ta na tsirga mishi, dariyar da takeyi bai hanata hararar shi ba
"Bawani nan..."
Murmushi ya keyi yana mika mata hannun shi daga inda yake zaune, karasawa tayi ta kama tana zama gefen shi kafin ta zare hannun nata tana daka mishi duka.
"Ouchhh... Adeee"
Ya fadi yana murza wajen dan yaji zafi sosai
"Ka zo ba zaka iya kirana ba Nawfal, ba sai kazo inda nake ba in ganka..."
Har lokacin murza wajen yakeyi
"Saboda ke fa na zo, yanzun nake. . .