Jikinta duk a sanyaye yake, tana tunanin yadda ta rungumo wannan hidima da ba ta taɓa yin irinta ba, duk da yake ta saba shiga a taimaka wajen shirya taro a makarantar su, inda take nazarin aikin kiwon lafiyar dabbobi, kuma lokaci zuwa lokaci idan ta samu hutu tana shiga aikin taimakawa a kungiyar Da'awah ta mata masu yawon wa'azi da faɗakar da 'yan mata da ke shiga shekarun balaga a makarantun sakandire da ba su tallafin audugar tare jinin al'ada ta mata.
Ƙarar wayarta da ke fitar da sautin addu'ar Hafiz Ahmad Suleiman. . .
Ma sha Allah. Allah ya ƙara basira da daukaka