Wani numfashi ya ja ya fitar da shi a wahalce kafin ya saki handle ɗin ƙofar tukunna ya ƙarasa inda su Tayyab suke, Zulfa ta soma tasowa ta kama hannunshi.
"Yaya Ummi ta haihu?"
Kallon Tayyab yayi. Bai furta ba, amma yanayin shi ya nuna cewa shima kalar tambayar da ke bakinshi kenan. Girgiza musu kai yayi, wani abu na mishi tsaye a ƙirji.
"Ku zo mu je."
Ya faɗi, muryarshi a dakushe. Ba musu suka bishi har ɗakin da Ummi take. Babban ɗaki ne da gadaje guda biyu a ciki. Sai kujerun zama har guda shida.
Ummi ce. . .