Karfe sha biyu dai-dai aka ɗaura auren Mami da Abba. Daga wajen ɗaurin auren, Dawud, Tayyab da Khateeb kansu tsaye gida suka dawo. Jikinsu sanye da manyan kaya na farar shadda ƙal da ita.
Ɗakin Mami suka wuce inda Zulfa da Mamin suke zaune. Da gudun shi Khateeb ya ƙarasa inda Mami take, riƙo shi ta yi tana matsa mishi ya zauna gefenta, ɗayan gefen zulfa na zaune.
"Mami an ɗaura... Mun gode sosai."
Dawud ya faɗi yana kallon Mami da ƙaddara ta jeho musu ita a rayuwarsu. Lokaci ya sa ta shiga zuciyoyinsu tai. . .