Tun farkon satin har ƙarshen shi Aisha ta rasa gane kan Auwal. Tun tana iya ƙoƙarinta wajen ganin yaran basu gane akwai matsala tattare da Abbansu ba har ta haƙura.
Gara ma Sajda. Don in ka ga murmushi a fuskarshi cikin gidan yanzun to Sajda ke bayyana shi. Tun da aka haifeta wata irin shaƙuwa ke tsakanin ta da Abban nata.
Har yanzun da canji ya same shi da Aisha ta rasa ko daga ina matsalar take akwai shaƙuwar nan duk da bata kai ƙarfin ta da ba. Idanuwa ta ɗauka ta saka mishi. . .