Tuni Binta ta kwashi haushi ta shige cikin gida, tana zuwa ta bude firji ta dauko ruwan sanyi ta fara daddaka. A haka Nabila ta shigo cikin sanyi jiki ta same ta, sai ta yi tsaye rungume da hannu alamar tana shakkun zama.
Binta ta dinga shan ruwan sanyi babu ji babu gani har sai da ta ji ta shanye sama da rabin takaicinta, sannan ta juyo cikin murmushin qarfin hali ta ce,
“A’a Nabila ki zauna mana”.
Hawaye ya zubo wa Nabila, tana rungume da hannu ta ce,
“Da kyar zan zauna Anti, tafiya zan yi”
Cikin sauri. . .