Shi kuma da yaga bai sami abinda yake so ba kawai sai ya canja kaya ya sake fitowa ya dawo falon ya zauna a kujerar da ke fuskantarta ya dauki filon kujera ya rungume.
“Nabila ta ce a gaishe ki.”
Ta san in ta sauke fishinta a wannan gabar zai yi ta mata gorin don kishi ta yi, saboda haka ta tura baki ta ce,
“Ina amsawa, dama ta daina wahalar da kanta aikoka ka gaishe ni, ai ni da ita kullum cikin gaisuwa mu ke…”
Ya tare ta yana dariya,
“Allah ko? Amma ko ni yanzun nan na dauki. . .
Ch hi