Sai kawai ta kawar da kai tana kallon windo mota tana qoqarin shanye hawayenta.
Ya kamo hannunta yana qoqarin juyo da ita don ta fuskance shi ya cigaba da more kallon kyakkyawar fuskarta mai sanya shi nishadi,
Da sauri ta janye jiki cikin dariya da farin ciki,
“Malam mai zance ai zaka saba qa’ida”.
Yana dariya ya shiga karkade hannu,
“Ayya! Uffararan, na sha’afa ne”..
Tana samu dariya ta fanshe mata hawaye.
“Mu dawo maganar mu, me ye ra’ayinki ga haifar mana yara? Ina son yara turmis, ina son masu sa ni farin ciki irinki.
Wannan karon. . .
Allah ya saka