Da wani irin farin ciki ta wayi gari, na farko, za ta je garin Kano. Garin da bata taɓa zuwansa ba, za ta ga Yaya Adam. Na biyu kuwa, za'a hukunta wanda ya kashe mahaifinta za ta ga danginsa kuma. Wannan ta sanya tun asuba zumuɗi ya hanata komawa bacci. Ta ɗakawa Amira da Jamila duka akan su tashi.
Fa'iza diyar Alhaji Mujahid, wacce ta kasance sa'arsu ta ja tsaki gami da cillamata filo a fuska.
"Kedai Allah Ya sauwake maki, ƴar kauye kawai. Wai ke baki iya komai a hankali ba?"
Humaira ta kai. . .
Halima k mashi