"Yayana na biyo."
Ya bi wurin da ta nuna da hannu, Bilal ya mike tsaye. Malamin ya yafito shi da hannu.
"Zo nan."
Hanjin cikinsa ya kaɗa, ya fito yana satar kallon Humaira yana harararta.
"Ya kuke da ita?" Malamin ya watso mishi tambaya.
"Kanwata ce, tana son zuwa makaranta amma Malam ya hana mata zuwa, ita ce ba ta jin magana."
Ya yi shiru yana dan nazari. Can ya bada amsa.
"Meyasa ba ya son mace da karatu? Alhalin ilimin mace mai amfanar duniyar ce ma gaba ɗayanta."
Sai lokacin Humaira ta soma magana cikin kuka. . .
A gode Allah yakara