Sun kulle sun dunkule sun zama abu daya, abokan sirrin juna, masoyan juna, kuma ‘yan uwan juna, kasancewar dukkaninsu ba su da wanda za su kira dan uwansu na jini, sai junansu.
Aisha na shara a tsakar gida wani yaro ya shigo, “Wai ana neman maigidan”.
Ba tare da ta juyo ba ta ce, “Ya tafi wajen aiki, sai karfe daya da rabi zai dawo.”
Yaro ya fita, can kuma ya dawo da ambulan mai fadi a hannunsa,
“Wai ga shi a ajiye masa, sako ne daga ‘post-office’. Aisha ta ce, “Toh”
Ta karba ta kai daki ta ajiye. . .
Sakallah khair