Tenure dinsu ya cika sun sauka daga kujerunsu na 'yan majalisar tarayya, 'yan rikon kwarya sun hau. Ana gab da yin zabe.
Yana zaune shi kadai watarana yana tunani. Hajiyarsa kullum girma kara hawanta yake, mijinta ya yi masa karah da duk wata alkunya da ta dace, ya sallama masa matarsa don kula da diyarsa. Ga Amina babu ranar tashi sai sanda Ubangiji ya nufa. Zaman asibitin nan ya ishe su duka daga shi har Hajiya har yarinyar.
Gara ta dawo gida a ci gaba da kula da ita a gida ko su ma hankalinsu ya tsaya wuri guda. Hajiya. . .