Flashback
Amina da Goggonta, tare da Inna Zulai da Goggo ta kirawo don ta taya ta jin wannan almara, ko kuwa rashin kan-gado da Amina ta zo mata da shi.
"In ban da rashin kan-gado irin naki Amina, ina hankalina zai kwanta kina kwance wani muhalli daban da nawa, alhalin na san ban yi miki aure ba?" Goggo ta fada cike da damuwa, muryarta a sanyaye.
Goggo Zulai ta ce, "Da ma a ce aurenki zai yi ne don ki kula da diyar da ya fi armashin ji."
Amina ta jefa wa Inna Zulai harara. . .