Hajiya da Ameena sun dade da yin bacci, har sun soma minshari. Sun kashe fitilu baccin gajiya kawai suke yi.
Ya kai hannu ya kunna wutar dakin, nan da nan dakin ya gauraye da haske. Da sauri ya isa gaban gadon ya russuna da gwiwoyinsa ya kama hannun Amina yana tattaba ta kamar wani abin ne ya same su na cutarwa.
Hajiya ta bude ido ta ganshi cikin wani yanayi da ta kasa fassarawa. Ya kuma ki bude baki ya yi magana, so yake ya ce da ita.
"Wace irin kara da kiyashi ki ka aura min haka ne Hajiya. . .