Amina da Goggo suna hira a yau, Goggo ta dubi Amina cikin damuwa, “Har yanzu lokaci bai yi ba da za ki kawo min miji Aminatu? Sai na fadi na mutu ban ga ‘ya’yanki ba Amina? Me ki ke nema a rayuwa haka? Na bi ki, na bi ki da duk abin da ki ke so da burikanki, sai yaushe ni za ki faranta min, ki cika min nawa burin a kanki?”
Hankalin Amina in ya yi dubu to ya tashi, ganin Goggo tana share hawaye. Ba ta san sanda ita ma idanunta suka yi rau-rau ba, ta. . .