Da daddare Gwoggo Indo na zaune tana cin abinci, Hamida na gefenta idonta na kan TV. Aina da ke ɗaki ta fito "Ni fa Gwoggo halin mutumin nan ya fara isa ta, wai idan yana gida ba hali in kira shi? Ni dai ban da kin matsa da tuni na kore shi." ta zauna tana tura baki. Gwoggo ta kwantar da murya,
"Kar ki kore shi Aina ki yi hakuri, ina gaya miki yadda matar tasa ta nema ta samu muma neman za mu yi, wuyarta dai ki shiga gidan, duk masu zuwa shi kaɗai ya zo da maganar. . .