Adai-dai lokacin da duk wannan ke faruwa, a lokacin ne kuma wata mulmulalliyar mota baka sidik kirar (Bently) mai kofofi hudu ta yi ‘parking’ a harabar gidan Makarfi. Tun kafin motar ta ida tsayuwa Maigadi ya karasa ya shaida masu cewa babu kowa a gidan duk suna babban asibiti, yarinyar gidan da yaron gidan ne suka suma.
A gigice Hassan Biu ya baiwa Direban dake jan su umarnin su nufi General Hospital. Tun kafin su isa Hajiya Hadiza ta fara kuka, ta narke Jikin Ambasada tace “ashe ma Allah ya rubuta gawar ta zan gani, Bashir?”
Yasa. . .
Muna godiya Allah ya Kara basira da xakin hannu
Intisaar na da tunani kamar ba yarinya ba, ki murza zaren ki har sai sun gane kuren su!
Wayyo Al-amin da Intisar