Ta zargi kanta ta tsani kanta duk a lokaci daya ta kuma kalubalanci zuciyarta da so da kaunar Al’ameen. Idanunta gab suke dasu tsiyayo da kwallar da ta kasa kwarara balle taji sanyi-sanyin azabtuwar da kirjinta keyi¸duk da haka tayi murmushi ta girgiza kai ta koma ta russunawa Dr. Abubakar Argungu ta ce,
“Don Allah Baban Anti Ihsan kada ka kara fadin wannan maganan. Alkawarine na riga na yi tuntuni ba abinda zai kara hadani da Jinin Haj. Nafi ko a Lahira balle aure? Da nasan ma Al’ameen dan ta ne wallahi ko gaisuwa...” sai ta. . .
Godiya marar adadi, Hajiya Takori.
Allah ya saka da Alkhairi
Masha Allah muna godiya
🤗👌🙏🏻