Ba tare da b’ata lokaci ba Baba Bashir ya fad’a musu duk abinda ya faru d’azu. Tun kafin ya k’arasa Baaba Talatu ta ce “zancen banza ma kenan! Ai indai gaskiya za a bi to haramun ne neman aure a cikin aure”.
Cikin b’acin rai Baba Bashir ya ce “waye kenan yake yi miki zancen banzan?? Sannan ban gane maganarki ta ‘neman aure cikin aure’ ba! Shin a tsakanin ni ko Madu waye kika tab’a ji ya cewa Usman ya bashi Maryam?
Shiyasa fa d’azu na kyale ku ban kira ku ba, duk. . .