Skip to content
Part 72 of 73 in the Series So Da Buri by Humaira Bulama

A hankali Mama ta lumshe idanuwanta wasu hawaye suna zuba. Daidai nan Ummu ta shigo, tana Isa gareta ta sa hannu ta yi hugging d’inta ta ce “congratulations”.

Ajiyar zuciya kawai Mama ta sauk’e daga nan d’akin ya fara cika da jamaa.

Banda hayaniyar mata babu abunda ke tashi.

Suna cikin hira suka ji d’aurin auren Jalila itama, nan take kowa ta hau tofa albarkacin bakinta wasu su ce “Allah shi k’ara” wasu kuma su ce “Ai ta ma yi sa a data auri Abdullahin, Mutum mai kirki da hankali da zuciyar nema wallahi ta tsinci dami a kala…”.

Kowa idan ya ga Abba a wajen d’aurin auren nan tashi d’aya zai san yau d’in fa yana cikin farin ciki. Ba shi kad’ai ba hatta su Granpa idan ka gansu fuskokinsu tap! Cike da annuri.

Ba a jima ba suka shiga parlourn Madu aka yi musu hotuna suka wuce bayan sun ce “nan da anjima in an d’an watse Abba zai dawo ya d’auki Amaryar shi da kanshi.”

Madu ya ji dad’in hakan dan dama shima ya gama deciding akan ‘ba sai an yi wani reton kai Amarya kamar wata Yarinya ba’.

Hakan kuwa aka yi.

Hudan ta so tsayawa amman awa uku kawai Aslam ya bata daga nann ya dawo ya d’auketa a cewar shi ‘gidan yayi mishi girma ya kasa shan ko ruwa tunda ya koma’.

Tunda ta ji haka dama ta b’aro jirginsa! Dan haka ta yi murmushi kawai ta girgiza kai tana mamakinsa.

Tunda aka idar da sallar Magrib Abba ya shirya tsaf!

Ana idar da sallar isha ya kama hanyar gandun albasa bayan ya samu Dad ya cika shi da kyar dan da farko rik’esa ya yi ya ce “akwai wani important aiki da zai taya shi dan Allah”.

Kamar Abba zai yi kuka haka ya yi mishi sai kuma ya ga Dad d’in yana dariya k’asa k’asa dan haka ya gano tsokanace!

Amman duk da haka sai da ya yi da gaske tukunna Dad d’in ya cika mishi riga ya wuce mota Dad d’in kuma ya nufi gidanshi yana dariya.

Yana zuwa ya tadda Madu zai shiga gida ya fito kenan daga masallaci dan haka suka shiga tare har parlourn Shuwa.

Nan Madu ya d’au waya ya kira Kaka da Baaba Talatu suka zo suka had’u suka yi musu Nasiha!

Daga nan suka sanya musu albarka.

Sai da suka zo tafiya ne Mama ta ji kuka ya taho mata.

Murmushi kawai Baaba Talatu da Shuwa suka yi daga nan Baaba Talatu ta mik’e ta k’arasa ta mik’ar da ita suka yi gaba Abba shima ya yi musu godiya da fatan alkhairi ya bi bayansu.

Da shi da mai aikin ne suka ja akwatunan Mama guda biyu da ta had kayanta a ciki suka kai mota suka sanya mata a booth.

Har k’ofar mota Baaba Talatu ta raka Mama ta bud’e ta saka ta a ciiki tukunna ta ce “Allah ya miki albarka”.

Tana mai rufe mata motar ta koma ciki.

Daidai nan Abba ya shigo ya rufe motar ya kunna ta, a hankali ya sauk’e ajiyar zuciya sannan ya juyo ya sa hannu ya jawota ya yi hugging d’inta wasu hawaye suna zubowa daga idanunshi.

Da sauri ta ce, “Abba mutane fa suna wucewa”.

Tana mai d’an k’ok’arin janyewa.

Bai cikata ba sai da ya yi niyya tukunna ya matsa amman still yana rik’e da hannunta yana kallonta ta cikin mayafin da ta d’an ja.

Murmushi kawai ya yi yana sauk’e wata nannauyar ajiyar zuciya kafin ya koma ya zauna rik’e da hannunta ya tada motar suka wuce.

Sai a sannan tukunna Baba ya share hawayenshi ya juya ya nufi cikin gidan Kaka yana ganin uku uku.

Tunda suka isa bakin estate d’in ta lumshe idanuwanta.

A hankali ya yi horn aka zuge makeken gate d’in suka shige ciki.


Direct gidan Granpa Abba ya nufa da ita.

Yana kashe motar ya d’an murza hannunta wanda tun d’azun da ya rik’e bai cika ba ya ce “Maryama”.

Sai a sannan ta bud’e idon ta d’an juyo ta kalleshi.

Murmushi ya yi ya ce “mu je ko?”
Jinjina kai kawai ta yi daga nan ta fara k’ok’arin fita sai kuma ta juya ta ce “hannuna”.


Sai a sannan ya d’anyi murmushi ya sakin mata hannun da kyar ta fita da k’ofar dama shima ya fito.

Suna d’an yin gaba ta ga yana shirin kama mata hannu!

Ba ma ta san wajen su Granpa za su je ba amman kawai ta yi gaba da sauri!

Murmushi kawai ya yi ya girgiza kai ya bi bayanta, daga nan suka jera suka shiga a tare.

A parlourn su Granpa na biyu
suka samesu suna jiransu gaba d’ayansu har Mommy da Dad.

Tana shiga Mommy ta mik’e ta je ta yi hugging d’inta tana farin ciki.

A gaban Granpa ta fara durk’usawa suka gaisa ya yi welcoming d’inta
sannan ta k’arasa wajen Gramma itama ta yi welcoming d’inta ta saka mata albarka tukunna Dad shima ya yi welcoming d’inta ya sanya mata albarka.

Daga nan Granpa da Gramma suka bata gifts d’insu.

Granpa ya bata fili a asokoro Grandma kuma ta bata sark’ar gold babba mai kyau da bangles d’inta da zobe.

Godiya sosai su Mama da Abba suka yi daga nan Dad shima ya bata nashi gift d’in kyautar mota har da Mommy aka hau godiya.

Sannan suka sake yiwa su Gramma godiya daga nan suka yi musu sallama da Allah ya kiyaye hanya dan sun ce jirginsu 3:00am zai tashi.

A ranar dattijawan unguwa suka zo suka zo suka bawa Madu hak’uri sannan da maganar ‘ya koma matsayinshi na mai unguwa’!

Da kyar kuwa da mugun kyar aka samu ya yarda ya karb’a saboda shi a ganinshi komai ya wuce sannan yanzu tsufa ya kama shi amman sam suka k’i amincewa suka ce “Ai su basu da wani mai unguwa wanda ya chanchanta sama da shi”.

Tunda Abba yake bai tab’a ganin nisan dake a tsakanin gidan Granpa da Gidan da zai zauna ba sai yau!

Allah Allah kawai yake su k’arasa.

Suna shiga Mama taga abun mamaki, har da wata k’atuwar heart a tsakiyar falon an yi decoration, ita kam abun ma ma sai ya bata kunya kar wani ya shigo ya gani.

Ruwan furniture da electronics kuwa kamar ba a san zafin kud’in ba.

A chan sama ma d’akinsu Abba ya yi decorating sosai da red hearts.

Ita dai Mama in banda murmushi ba abunda take yi dan har ga Allah abun ya burgeta.

Idanuwanta suna kaiwa kan akwatuna dozen a take ta b’ata rai!

Da sauri ya kauda kai yana d’an murmushi.

Cikin rashin jin dad’i ta ce “Abba cewa fa na yi ka barshi.

Ka san za ka yi shine mu kuma ka hana mu yin kayan d’aki?”.

Da sauri ya sa hannu ya toshe mata ba ki ya ce “Maryam wallahi ba ni da energy d’in arguing yanzu, ba ri mu yi sallah ko? Mu ci abinci sai mu yi magana.”

Da “to” kawai ta bishi, tana ta faman fushi suka yi sallar suka ci abinci.

Za ta ci gaba da mitar ya ce “Bara inyi wanka sai ayi min mitar ko?”.

Ya fad’i haka yana tattare wajen ya yi waje da sauri yana mamakin Mama da mitar ta har yanzu ashe tana nan.

Itama wankan ta yi ta nad’a laffayarta bayan ta chanza kayan da ta zo da su a cikin akwatinta.

Tana cikin nad’a laffayar ya shigo, ya tsaya a bayan ta. Ko juyowa bata yi ba
ta ce “Yanzu inda nice na nace sai na zo da kayan d’aki nasan ba za ka ji dad’i ba amman ni kalli ka yi lefe bayan an riga an gama magana,
sai ka ce wata Yarinya…”

A hankali ya juyo da ita ya ce
“Wallahi bana gane abubuwan da kike fad’a!

Na gaya miki ba ni da energy d’in arguing…”

EARLIER
Wata razananniyar k’ara Umma ta saka mai had’e da ashar kamar wata mahaukaciya!

Jalila kuwa gefe guda kawai ta koma ta zauna dab’ass!! Ta k’ame a waje guda sai kuma hawaye suka hau zirya wani na korar wani ba k’akk’autawa.

Tabbas ko jiya sai da Abdullahi ya kirata, da ta k’i d’auka ya yi mata message yana cewa “Gobe in shaa Allah zai yi mata kyauta surprise
na ban mamaki.”

Tsananin tashin hankali da bak’in ciki suka sanya kawai ta tafi ta sulale ta sume a wajen.

Da gudu Umma ta k’arasa kanta ta hau jijjigata amman sam bata motsa ba!

Sai da Hansai ta d’ebo ruwa aka shek’a mata tukunna ta farfad’o, suna had’a ido da Umma ta fashe da kuka.

Kasa cigaba da kallon idon nata Umma ta yi, ta mik’e kawai ta ja hannun Hansai suka shige chan k’uryar d’aki.

Jakarta kawai ta d’auka ta cewa Hansai “yi mini kwatancen Dajinma!”.
A zabure Hansai ta ce “Ke!!! Sadiya? Dajinma?? Gaskiya ni kam ba da ni ba!
Har me ya yi zafi haka?”.

Cikin katseta da sauri Umma ta ce “komai ma ya yi zafi!!! Haba Hansai!
Sai kace ba kya gani?

Ki duba kiga Maryam da Huda sun fini ta ko wacce hanyasannan tsabar Bashir d’an kutumar bura uba ne.

Kalli a yadda ya aurar da Jalila
kuma auren ma da talakan tukuf!!

Dan nasan had’in sa ne wanan, shegen tsoho ya tsaneni ya tsane y’aata!

Tun da ya kafa mata k’ahon zuk’a sai da ya yi mata auren dolen tukunna hankalinsa ya kwanta!

Ai kuwa wallahi ba zata sab’u ba! Ko sadakin ba za mu karb’a ba wallahi sai ya sakar mini y’ata, ban haifeta dan ta je ta auri talaka ba wallahi.

Ki yi min kwatance ko kuma In tafi in nema. In ba haka ba mutuwa zan yi
kin san Allah takaice da bak’in ciki sai sun kasheni!!!!…..”

Cikin son fahimtar da ita Hansai ta ce
“Sadiya wajen nan ban da mayu da aljanu ba abunda suka cikashi!

Kuma fa sai kin yi tsirara tukunna zasu saurareki!

Ke kad’ai a tsakiyar daji.”

Da sauri Umma ta ce “zan iya!! Kwatance kawai nake buk’ata
ki yi mini idan na je ko me aka ce min inyi zan iya muddin zan ga Maryam da Huda a k’ark’ashina sannan basu fini da komai ba! Haba mana! sun fi kowa ne? Kalli mazajen fa da suka aura.

Hansai zuciyata zata buga ki yi min kwatance in wuce da wuri tun kafin Maryam ta tare a lalata auren sannan a sauwwak’ewa y’ata wannan auren talakan tukuf d’in ta auri Arshaad.”

Ajiyar zuciya Hansai ta sauk’e kafin ta ce “Sadiya ni a ganina gara dai aje wajen y’an saffa saffa da aka saba
su san abun yi, Dajinm….”

Wani uban ashar Umma ta k’unduma kafin ta ce, “Hansai kar ki kashe ni!

Malaman Ina ce sune suka bamu wannan hayak’in muka yi muka turnuk’e ko Ina?

Na tabbatar ya shiga gidan Madu ta shak’a kowa ya shak’a ke har kwandila na tabbatar ya zagaya amman kinga an fasa auren Maryam da Abba?

Sannan malaman ba su ne suka yi ta amshe kud’ad’en mu akan batun Jalila da Arshaad ba?

Kin tab’a ganin Arshaad ya yiwa Jalilan koda message ta waya? Dan haka kawai ni kinga ki rabani da zancen malaman nan ba zan iya ci gaba da kwasar takaicinsu ba duk y’an damfara ne!

Gara kawai ki had’ani da Aljani ko Maye wanda na san ba cuta ba cutarwa!!

Yi min kwatance maza maza inje ayi a gama kafin Maryam ta tare”.

Ta k’arashe maganar rai a masifar b’ace a gaggauce tana gyara ruk’on jalarta da mayafinta.

Ajiyar zuciya Hansai ta sauk’e sannan ta kalleta ta ce “Zan iya kaiki wajen dan ba lallai ki gane ba, nima k’awarnan tawa na tab’a rakawa
kuma zan gane. Ni na yiwa Mijina ita kuma kishiyarta wadda ta b’ace b’at!! Har yau babu ita ba labarinta kamar yadda ta buk’ata.”

Wani shu’umin murmushi na tsantsar jin dad’i Umma ta yi.

A hankali Hansai ta ce “Muje in rakaki,
sai ke ki shiga jejin ni kuma in jiraki a bakin kogin.”

“Na gode Hansai” Umman ta ce
fuskarta tana baiyyana tsananin farin cikin da take ciki.

Laraba da Jalila suna parlourn a yanda suka barsu suka zo suka wuce su.

Ce musu kawai suka yi “bara su je su dawo” Ko Laraban basu gayawa inda suka nufa ba suka fice suka kama hanya.

Sai da sukayi mota uku da mashin biyu
tukunna suka isa bakin kogin daidai ana kiran sallar Magrib.

Naira hamsin suka biya mai kwale kwalen ya tura su ya kaisu bakin dajin
Umma ta shiga cikin dajin.

Hansai kuma ta zauna a wajen itada mai kwalekwalen zaman jiran fitowarta da alk’awarin zasu bashi naira d’ari biyu idan ya jira ya fitar dasu.

Sauri sauri Umma take tafiya ita kad’ai a cikin dajin dan tana so su yi su gama su koma koda wani d’an k’auye ne su kwana a hanya saboda tasan tabbas komawarsu a yau ba zata yiwu ba.

Wani kalan murmushi ta yi sakamakon hango dakali a zagaye mai kewaye da ruwa a tsakiyar wasu dogayen bishiyu guda bakwai.

Already Hansai ta fad’a mata yadda zata yi dan haka ta kwab’e tik! Hatta zoben hannunta da y’an kunne sai da ta cire ta ajjiye ta cire takalminta ta nufi dakalin tsirara haihuwar Laraba.

Tana zuwa ta d’auki itace mai d’an tsini ta chaka a tsakiyar hannunta sannan ta bi ta zagaye wannan ruwan da yake kewaye da dakalin tana mai d’iga jininta a cikin ruwan!

Tana gama zagayewa ta tsallake ruwan ta hau ta d’ale kan dakalin ta zauna.

Wata firgitatciyar k’ara aka yi da ta sanya jinta ya d’auke d’iff gabad’aya!

Hatta Hansai da mai kwalekwalen sai da suka ji dan haka a firgice mutumin ya ce “Kai! Kai!! Kai!!!

Maza mu bar nan basa k’aunar jininta!! Kar mu je abun ya shafemu, bara mu juya da sauri.”

Da sauri Hansai wadda itama k’arar ta mugun firgitata ta ce, “Ban gane basa k’aunar jininta ba? Kamar ya?”

Kallon ta mutumin ya yi kafin cikin b’acin rai ya ce “Au ku baku san sharud’an wajen ba kuka kwaso k’afa kuka taho?

To ni kam ba da ni ba gaskiya!
Ba za ki sa a had’a da ni ba.”

Yana gama fad’in haka ya fara k’ok’arin juya kwalekwalensa.

Kuka Hansai ta saka kafin ta ce “Malan y’ar uwa ta fa?

Ya za ai In tafi In bar y’aruwata??”

Tsaki kawai ya yi kafin ya ce
“Kin san Allah in kika b’ata min rai kika yi min taurin kai har wani abun ya shafeni sai na kasheki!!!

In kuma kina son tsira tou
ki ja bakin ki ki yi shiru mu bar nan tun kafin a jiyo mu!!

Idan Allah ya kaimu gobe da sassafe na san basa nan sai mu zo mu d’auki gawarta!”

Hansai na shirin yin magana cikin kuka wata mahaukaciyar iska ta hankad’o su daga su har kwalekwalen nasu!

Da kyar ta tsayar da su a tsakiyar kogin ai kuwa da mugun sauri mutumin ya cika inda suka kakkama saboda kar su zube ya hau tuk’a kwalekwalen ya kaisu bakin rafin.

Ko tsayawa k’ullewa bai yi ba
ya fita da guda ganin haka yasa itama Hansai ta raka shi da nata gudun
dan ba k’aramin tsorata tayi ba.

A gidansa inda ya nufa ta kwana bayan sun sha artabu saboda da cewa yayi ba zata bishi ta ja mishi jalala ba dan ya lura dak’ik’iya ce.

Kamar yadda ya yi mata alk’awari
washegari da sassafe ya nemo mutane suka nufi wajen!Har ita suka shiga wajen.

Anan kan dakalin suka hango Umma kwace k’afafuwanta a cikin ruwan ta gaba. Hannayenta ta gefe da gefe duk a cikin ruwan da yake zagaye da d’an dakalin.

Gashin kanta kuma yana tab’a ruwan ta baya.

Da sauri suka k’arasa inda take suna isa Hansai ta fashe da kuka a mugun tsorace ganin an kwakule mata idanuwa.

A cikin Mutannen ne wani ya cire y’ar sharar jikinsa suka rufa mata suka yi waje da ita.

Har aka isa gidan Mutumin in banda kuka ba abunda Hansai take yi duk a tunanin ta mutu amman ana zuwa gidan da aka kawo ruwa matar mutumin tana wanke mata fuska sai suka ji tana magana k’asa k’asa.

Da sauri Hansai ta matsa sosai ta fara yi mata magana tana cewa “Sadiya me kike cewa?? Sannu sannu Sadiya, mai ya faru dake haka?”

Sam amsar da take bata babu kai!

Ita kuma Hansai ta dage sai magana take yi tana d’an murna ganin y’ar uwar tata nada sauran rai.

Matar ce ta ce mata “Ba fa zata fahimceki ba.

Babban abun mamaki ne ma da aka sameta da rai, sai dai kuma ina yi mata takaicin a haka zata k’are rayuwarta
dan sam ba zata tab’a yin hankali ba.

Allah kad’ai ya san me da me ta gani
sannan kin san suna d’auke hankali da kwakwalwa bayan sun cire ido.”

Cikin tsananin fashewa da kuka Hansai ta ce “Na shiga uku!!!

Dan Allah idan akwai mai Magani duk inda yake ki yi min kwatance In kaita wallahi k’anwata ce.”

Sai da matar ta d’an k’ura mata ido tukunna ta sauk’e ajiyar zuciya kafin ta ce,

“K’anwar ki ce amman kika kawota ga halaka?

Wacce iriyar yaya ce ke? To bari kiji in gaya miki tunda muke a k’auyen nan
kafuwar shekaru kusan d’ari!

Ba a tab’a yin wanda ya shiga wajen nan basu k’aunaci jininshi ba ya fito da rai!

Wasu kuma da aka k’aunaci jinin nasu ma za su je su dawo k’alau daga baya kuma kiga hankalin ya tab‘u!

Balle ita da basu k’aunace ta ba tunda gashi har idanuwan sun cire ai kawai
ku rungumi k’addara dan ni bansan wani me magani ba gaskiya.

Ku samu ta warke daga wannan radd’ad’in kwakulewar idon, ku yi jinyar haukarta.

Idan iyakar abunda ya sameta kenan.”

Tana gama fad’in haka ta mik’e ta yi gaba.

Hansai ta yi kuka ta yi kuka kafin daga baya kawai ta sa aka taya ta ta kinkimi Sadiya bayan an sanya mata kayanta ta d’aura akan mashin.

Suna isa wani k’auye ta ci sa’a ta samu motar kano direct!

Shata ma tayi ta ce in sukaje gidan zata shiga ta d’auko masa kud’insa saboda Sadiyar ta samu ta mik’e.

Har k’ofar gida ya kaisu.

Sai da ta rufe mata fuska da d’ankwali tukunna ta shiga ta kira K’asimu da Laraba.

Da taimakon drivern aka shigar da ita
K’asimu sai faman sababin tambayarta yake yi.

Laraba kuwa tun daga yadda taga fuskar Hansai da kuma Sadiyar gabanta ya fad’i!

Shiyasa ta ma kasa maganar ko iya kama Sadiyar ma bata yi ba, yadda take a sandare ne ya sanya ta yi tunanin ko mutuwa ta yi shiyasa ana shiga gidan tun kafin a gama kwantar da ita akan tabarma ta fashe da kuka.

Jin kuka yasa Jalila wadda tun jiya Laraban ta b’oye ta a d’aki ta cewa su Baaba Talatu ‘ta gudune ita da Sadiya’ ta fito!

Tana hango Sadiyar a kwance ta tafi jikinta ta fad’a ta fashe da wani matsanancin kuka.

Hansai bata tanka su ba sai sake kiran Junaidu da tayi ta ce masa “sun iso yanzu ya zo” sannan ta je ta duba d’akin Amarya taga da sakata
tukunna ta dawo inda suke ta tsugunna.

Daga K’asimu har Laraba babu wanda ya iya tab’a Sadiya dan shima K’asimun zuwa yanzu ya fara tsurewa
sakamokon ganin da yayi ko motsi Sadiyar bata yi.

Tana tsugunnawa taji ana tab’a k’ofa dan haka ta je ta tambaya “waye?”

Ajiyar zuciya ta sauk’e jin Junaidu ya ce “ni ne”. A hankali ta bud’e mishi.

A hankali yad’an gaisheta
sannan ya hau tambayarta “mai ya faru? Ina Umman nasu!?

Sun tafi tun jiya wayar su bata shiga. Mai ya faru ba dai hatsari suka yi ba ko?”

Maganarsa ce ta katse sakamokon hango Sadiya a kwance a sank’ame!

Da kyar Junaidu wanda k’irjinsa ya hau dukan uku uku ya samu ya k’arasa wajen ya tsugunna ya yaye mata fuska!

Wani wawan tsalle K’asimu yayi had’e da ihu ya fad’a kan Laraba tsabar tsananin tsoro.

Da sauri shi kuma Junaidu ya kauda kanshi gefe ya runtse idanuwanshi wasu zafafan hawaye suna zubo mishi
daidai nan Hansai ta k’araso wajen.

Cikin kuka Laraba wadda ta samu ta ture K’asimu daga kanta da kyar ta ce
“Hansai garin yaya haka ta faru?
Mai ya sameta haka ba ido? Su waye suka kashe min Sadiya?” Ta k’arashe maganar tana sake fashewa da wani matsanancin kuka.

Tiryaan tiryaan haka Hansai ta zayyano musu duk abunda ya faru bata b’oye komai ba sannan ta ce “Tana da rai bata mutu ba, ina ga yanzun bacci tayi.”

Cikin tsanannin b’acin raii Junaidu ya rufe ta da fad’a kamar y’arsa, babu abunda ya fi b’ata mishi rai irin wai ‘wajen mayu da aljanu suka je!

Ya jima yana bala’i yana hawaye kafin ya mik’e a mugun fusace ya fita.

Jalila kuwa in banda kiran sunanta tana tattab’ata ba abunda take yi.

Junaidu bai yi minti ashirin ba ya dawo gidan da wasu mutane kana gani kasan Likitocine. Su suka d’auketa daga nan ya cewa Hansai ta biyo shi.

Bai dawo ba sai washe gari shi kad’ai ba Hansai.

Jalila da Laraba ya tarar a parlourn.

A hankali ya zauna yana kallonsu
Jalila ta rakub’e tanata faman kuka abun tausayi.

Da kyar ya kauda idonshi a kanta yana jin tsananin tausayin ta daidai nan K’asimu ya shigo ya nemi waje ya zauna sannan ya ce “Gani dan albarka ya ake ciki?”

Sai da ya sauk’e ajiyar zuciya tukunna ya ce “Umma bata mutu ba!

Amman halin da take ciki gara mutuwa.

Ta samu tabun hankali sannan idanuwanta babu kuma k’afafuwanta sun shanye.

Yanzu dai na turasu Cairo ita da Hansai, za a yi mata aiki a chan daga nan ta d’an dade ta kafin su dawo…”

Shiru, yayi yana jin zuciyarshi tana tafarfasa kafin ya mik’e ya k’arasa wajen Jalila wadda take kuka wiwi ya zauna sosai a gabanta.


A hankali ya kamo hannunta ya fara magana “Jalila sai dai hak’uri,
kuka ba zai yi maganin komai ba, mu bita da addua kawai da fatan Allah ya bata lafiya.

Kuma ina so ki yi hak’uri sannan ki cire taurin kai, ki rungumi Mijin da aka zab’a miki!

Ki nutsu ki yi hankali Jalila dan girman Allah, Umma kad’ai ta isar miki ishara.

Ba komai kake sakawa a gaba ka samu ba.

Dan Allah dan Annabi Jalila ki koma kamar Jalilan ki ta daa yadda kike lokacin da muke a hannun Mama kafin dawowar Umma cikin rayuwarmu!

Ki duba dai ki gani tsarin da kuke kai ke da Umma ba dai dai baneba sam!

Na fad’a muku na yi nasihar har na gaji daga ku har Anty Zainab wadda ita yanzu Allah ya taimaketa ta gane gaskiya.

Ki bud’e idonki da kyau ki duba ki gani
shin da ku da su Mama waye ya ci riba yanzu?

Kinga fa tun a duniya Ubangiji ya nuna muku iyakarku.

Ki hak’ura da Arshaad, ki hak’ura da So da Buri Jalila ki hau matakin gaskiya za ki ji dad’i a yanzu da gaba.

Ki yi hak’uri ki tare a gidan Mijinki.

Na so in ba shi gida babba mai bene da komai amman furr ya k’i, haka dole na hak’ura na ba shi k’arami mai d’akuna biyu da toilet d’aya da parlour har da tsakar gida saboda ya ce shi kad’ai zai iya affording dan ya tabbatar min ‘tabbas zai dinga biyavna kud’in haya’
Jalila irin wannan Mijin mai wadatachchiyar zuciya shi a ke nema, ki duba fa kiga ya san da zancen ki
ke da Auwal ya san komai amman ya ce ‘ya ji ya gani’.

Mahaifiyarshi ma ta ce ‘ta ji ta gani’,
What more could you ask for daga bawan Allah nan??.

Kar ki damu na yi miki kayan d’aki da kayan kitchen na gani na fad’a, ki yi
hak’uri ki daure Jalila pls.

Mahaifiyar shi tana chan hankalinsu duk a tashe!

Shiyasa na je na same su na ce ‘anjima da yamma su zo a mik’a ki gidanki’.

Ki fad’a min ko nawa kike so zan ba ki jari. Duk abunda kike so don’t ever hesitate to ask me!

Dan Allah Jalila amman ki yi k’ok’ari ki gyara halayenki dan zaman gidan aure daban yake da zaman gida.

Ba ki da wanda zai gaya miki gaskiya sama da ni…”

Nan ya yi mata Nasiha mai tsananin rashi jiki.

Ya k’arashe da “Allah yayi miki albarka. Anjima kafin a kai ki ki je gidan Kaka Baba ya ce ‘ki je ki same shi suna son ganinki’.”

Cikin tsanannin kuka Jalila ta fad’a jikinsa tana cewa, “Ka yi hak’uri Ya Junaidu.

Ka bawa su Mama hak’uri. In sha Allah zan chanja zan yarda.

Dan Allah ku tayani da addua ni kaina bana son in sake komawa waccar Jalilar saboda in banda tsananin k’unci da tashin hankali da wulak’anci ba abunda na tsinta.

Hankalina ya fi kwanciya a lokacin ina wajen Mama babu kyashi ba hassada ba komai.

Dan Allah Ya Junaidu ka tayani bawa su Huda hak’uri wallahi na tuba.”

Hannu yasa ya rungume ta shima yana hawaye.

Sun jima a haka tukunna ya mik’e ya mik’ar da ita tsaye ya kama hannunta ya ce mata.

“Ta shiga d’aki ta huta zuwa lokacin da Anty Zainab zata zo ta tafi da ita gurin su Baba”.

Dan sam baya son barinta da su Laraba gudun kar su sake hargitsa mata lissafi.

Da “to” ta amsa sannan ta shiga ciki
dan itama tana buk’atar hutun.

Sai da ya ga ta kwanta tukunna ya juya ya fita ya yiwa su K’asimu sallama ya fice.

<< So Da Buri 72So Da Buri 74 >>

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
2
Free daily stories remaining!
×