Skip to content
Part 6 of 15 in the Series Tana Kasa Tana Dabo by Hadiza Gidan Iko

Tun a mota Sameer yake jaraba Kiran wayar wasila Amma har yanzu baiji wayar ta shiga ba sai ma shegiyar matar Nan Mai kaifin muryar tsiya da take ta fada mishi wannan layin a kashe take sai dai ya sake Kira Lokaci na gaba.

Haka ya iso majalisar tasu inda ya iske duk mutanen su sun hallara motoci ne fal a wurin na mate din su Wanda Suke cikin garin katsina wanda Ake haduwa ayi fira a Sha shayi na Yar buta kasancewar kowanen su Yana da Aikin Yi Mai kwari . Kuma Masu budewar ido akan Rayuwa musamman ga mata don Mafi yawan su Yan YA ZA AYI ne duk da suna da Abun hannun su kam.

wasu Aikin banki wasu Yan kasuwa wasu Kuma kaki ne irin su Sameer inda wasu Kuma seabil difens ne kowa dai da irin Abinda Allah ya nufe shi da Yi.

Ya faka motar ya fito Yana hango su sunfi su goma Sha suna Ganin shi Suka fashe da Dariya suna Fadin.

“Marmari Daga nesa SOJA ikon Allah SOJA mijin Farida fara mace Daya wacce ta zarce Dubu. Mace Mai juya Maza Maza Maza a hannun Mata.

Suka Kuma kwashewa da Dariya.

Shugaban majalisar tasu wato garba Abubakar Wanda a kofar store din AJIYAR kayan su ne Ake kafa majalisin ya tsiyaya Ruwan shayin Yar butar Yana Fadin.

“K’araso mutumi na kasha wannan hadin irin naku ne Maza in ka Sha shi yau sai anyi Maka kuka don batun bacci dai yau Babu shi. Sameer ya zauna Yana Fadin

“Kuce yau iya shegen majalisar Nan a Kaina kuka shurya shi.

“Kai manta da mutanen Nan Mutum na karbi shayin Nan Yasin Nima Nasha shi Ina son na gwada don mutumin ka Mai naira yace babu karya yaga zahiri don till down yayi.

“Yanzu shi wannan Yar yarinyar yayiwa till down don bashi da Imani? Cewar Salisu sico.

“Kai wa ya fada Maka? Ai wannan lallaba Kaya na nake in itace nashawa Abun Nan ai har makota sai anjiyo mu Kuma ni ba zan nuna Mata wannan muguntar ba kudi na na biya na Kuma gamsu da yadda nayi tunda na Siya an siyar min meye na Jin tausayin? Ai malam in kana son till down ma kar ka neme shi ga Yar yarinyar wacce Bata Goge ga harkar ba gara ka samu gogaggiya wacce in ma za a kwana Bata da matsalar shiga Ruwan zafi Amma Yan Mata wacce in ka taba Dole a Nemo Ruwan zafi ai sai dai keta zata sa kayi musu wannan zullar.

Cewar Alhajin naira.

“Wai akan wata yar Iska ka sauke nauyin ka ne a gwajin maganin Nan Mai naira?

Sameer ya tambaye shi Yana son Jin kwab…

“Hahahaha Alhajin naira ya gaggabe da Dariya Yana Fadin

“Ai ban yarda na kwana ban sauke nauyi na ba akan Mai kayan Dadin Nan don Wallahi a Raina ta zauna dam naji matukar ban neme ta Akwai matsala. Yadda kaji shawarmar Nan to haka Nan take.

“Wai wasilar Nan kake nufi Mai naira?
Sameer ya tambaya da sauri don Wani Abu yake ji Mai kama da mishi Allah yayi shi mutum Wanda Baya son tarayya akan komai bare mace ace sunyi tarayya da Mai naira Wanda ya San maye ne duk yafi sauran.

“Kai maza ai Yasin matar Nan gama Hawa ce Wallahi ni ko ya akayi ma sokon mijin ta ya kasa Nemo kudin da zai killace Abar sa a gida ya barta tana Shan Wahala? Ai ban runtsa ba Ranar da na karbi lambar ta sai da na shimfidar da ita a kirji na samu lafiya wannan wasila Allah yayi Mata wasila Kam wannan idan ta jika Anya ba zanyi WUF da ita ba? Wallahi mace ce Sosai kinko ne dai ya so kashe ta Amma nayi nufin tayar da ita don zataji wanka har ma shawarma da bogar nace ta Daina Yi ita ba kalar Rana bace na linka ribar da Ake Samu zan bayar sai dai nace ayi min Wanda zan ajiye a mota Ina ta bawa.

Kwana biyu Babu Abinda nake marari irin mu koma tafki Amma Ina Jin shegen mijin ya kasa ya tsare don bamu Sami haduwa ba wayar ta ma a kashe take kasan talaka da Shegen ikon tsiya.

Gabadaya Sameer yaji wasila ta fita a Ranshi duk da mayatar bariki da yake da ita Yana da kishi ba komai yake son suyi tarayya a so ko samu ba.

Mai gemu Wani Mai masifar son Matan tsiya Wanda ya kasance canji ne sana ar sa kudi Kam har na wofi Yana samun su Shima Kuma maye ne na Sosai a mata don ya zarce Mai naira tamkar Kuma Mai Asiri duk macen da ya nufa da son ya lalata ta sai ya samo kanta sai dai in Basu Yi ido Hudu bane.

Ya dauki kofin shayin shi ya Kai baki Yana Fadin.

“Ni kuwa wannan Mai kayan Dadi da kake magana mai naira banzo majalisar Nan ba ne Ranar da ta zo halan? Wane irin kayan Dadi kake magana.

“To Dan iskan karshen Duniya boga da shawarma nake nufi Kai da ko rijalai suka Daura Dan kwali yanzu ne zaka Rikice bare Nisa u suyi Maka fari da ido yanzu ne za a Gane kowaye Kai Babu Ruwan ka da ita Kaya na ce na Kuma Hana ta kula kowa kaje can ka nema a Gaba.

“Ai yadda naji kana ta Fadin yadda till down Dinka da ita naji Ina zan same ta.

“Ba Kuma zaka same ta ba Mai gemu an Riga ka biya don na San zaka iya zuba Jarin da ni ba zan iya Zubawa tunda ka daurewa asara katara.

Sameer ya Mike Yana Jin duk firar ta ishe shi ya gama da babin wata ABA wai ita wasila.

Ya wuce Yana musu sallama ya figi motar shi ya wuce gida Yana Bak’in cikin Abinda yayiwa Farida da tana gida da ba haka ba.

Ya Isa gida ya watsa Ruwa cikin shi Kuma ya Soma Kiran Ciroma yunwa Dole ya fita yayi take away ya dawo gida

Sai dai me? Yana kwanciya Abunda ya shawo a cikin shayin Nan da Ake bashi Labari ya Soma tambayar shi. Yana zaune Yana yamutsa Sumar kanshi Yana numfashi har ya samu bacci ya dauke shi.

Gari na wayewa ya dauki hanyar Kaduna zuwa gidan Yaya dauda yaga yadda zasu kare in tayi Ruwa Rijiya in Kuma ta k’afe Masai don ya Rasa ta hanyar da zai iya magana da Farida tunda ga wayar ta a gida ta bari . Bashi da Wanda zai Kira ya hada su. Don haka sai kawai yayi Shan giyar kusu ya nufi garin kaduna ya tunkari Yaya daudan da nufin ya karbo matar shi tunda a sati Daya Haj tayi magana gashi yau har kwana Tara.

*****

Ranar da suka iso garin kaduna Yaya dauda Asibitin kud’i ya zarce da Farida aka shuga Bata kyakkyawar kulawa inda ya dauko matar shi Anty lubna mace Mai kirki da son Yan Uwan mijin nata. Duk da gizagon dauda da tsare gidan shi zaka Sha Mamaki idan kaga yadda Anty lubna ke jan Zaren ta Kuma dauda Yana Nan Nan da matar sa mace ce wacce ta San kanta ta Kuma iya mu Amala da mutane ta ke Kuma bi da mijin ta duk abinda yake so ta Kuma bar Wanda Baya so shine kawai Sirrin da ke tsakanin su Amma a gefe wasu suna Ganin lubna ta San hannun ta ne koma tana biye biyen mayakan zaune wato bokaye to Babu ko daya Yi nayi ce bari na bari sai Kuma sanin wacece ke Shima Yana kara tasiri matuka Gaya a Rayuwar Aure Amma Sirri dai kam biyayya ce farko.

Anty lubna ta tsaya a kan Farida a kwana Biyu ta Dawo hayyacin ta har fari ta Kara kafin aka sallame su Suka wuce gidan Yaya dauda Dake jaji Wani irin gida Mai cike da matsara duk sojoji Kuma Wani irin gida Wanda komai hadiman gidan sojoji ne inda suka Babu shiga Babu fita Saboda komai akwai hadiman gidan shiyasa farida Bata son ziyartar gidan Yaya dauda tun lokacin Yan matancin ta duk da son da Anty lubna ke Mata da son tazo jaji Amma Saboda wannan dokar ta gidan yasa Bata son Zuwa sai fa Dole sai gashi yanzu an figo ta an kawo ta ana mata Wani iko da Rayuwa ita da Bata Kai k’arar mijin ta ba bare ace hakkkin ta za a kwato Mata a Barta a gidan ta mana za a Wani rarumo ta gari ya gari har kaduna don dai Mulkin mallaka wai biyan bashi da Ya’yan kishiya?

Suka iso gidan inda aka sauke ta a D’akin ta na musamman yayin da Anty lubna ke Mata girki na musamman saboda lnganta lafiyar jikin ta musamman Ma da aka ce tayi b’arin ciki sai ya zama Abincin ta na musamman ne.

Bata taho da Kaya ba don Haka Yaya dauda ya tura lubna kasuwa ta samo Mata Kayan sakawa sai ga Kaya masu Daraja dogayen Riguna da atamfofi da lass har da takalma . Kai ba ita kadai ba hatta Saddam da Hanan Kaya Anty lubna ta Tara Mata a gaban ta tamkar dai tazo kenan ba zata Koma . To in ba haka ba ita da akace sati Daya ta koma shine Ake Tara Mata wadan Nan kayan kamar Yar Gudun hijira?

“Wai Anty lubna meye na Tara kin kayan Nan haka? Nifa kwana bakwai haj tace wa Yaya dauda na koma Kuma Kuna ta Tara min wasu Kaya sai kace nazo zama saboda Allah ko dai Wani Abu Yaya dauda yake nufi ne ?

Anty lubna tayi murmushi tana Fadin
“Farida Wallahi na jima ban ga Dan Uwan Da yake son Yan Uwan sa kamar yayan ku ba. Musamman ma ke da kike ke daya mace a cikin Maza Hudu . Bana tunanin Yayan ku Yana da wani Abu a Ranshi a game da ke kar ma ki kawo wannan a Ranki ke kin San ko Baki zo ba zai iya aike Miki da fin wannan.

“Har yanzu Anty lubna Baki San wancan mutumin ba kina tare da mutum Amma Baki San Halin sa ba makahon so ya Rufe Miki ido komai yayi daidai Ne a wurin ki ni nasan akwai wani Abu a k’asan ransa to ni fa bana son yayi min shisshigi ana shiga tsakanin Mata da miji ne?

Anty lubna ta zuba Mata ido Amma ta kasa cewa uffan sai ma mikewa da tayi tana fadin

“To Farida ni dai Sako ya bani kuma na isar da sakon shi in kina da magana wannan bana tsakanin ku ku kashe ku Rufe tsakanin ku ni dai kar ki ga laifi na.

Farida ta kirne fuska Bata kuma kallon Anty lubna ba har ta fice ta bar Farida tana hararen Kayan.

Anty lubna ta samu Yaya dauda a d’aki tana Fadin

“Daddy wai lafiya kuwa Farida? Ni kaina nayi Mamakin tafiyar Nan Babu shiri Babu kayan Sakawa?

Ya bude hannunwan shi Yana Rungume lubna Yana Fadin

“Baki ga jikin ta duk shacin duka ba? Wai fa Sameer ne ya Dake ta da belt Babu Wanda ya San Hakan sai fa Saddam ne yake fada Dama Kuma yasha kamata ya jibga Amma da nace zan dauki mataki sai haj tace Babu Ruwa na kar na ce komai to Amma a wannan karon sai na nunawa Sameer shi k’aramin Dan iska ne shiyasa nayi Hikimar tahowa da ita Nan gidan . Ki taimake ni ki Taya ni Saka ido akan Farida . Banda fita ko Ina kuma kar ki sake ki bari ta dauki wayar ki don Bata da mutunci akan wannan Dan iskan yaron to ni da su zan ga Mai taurin Kai da iya jan Rigima Kuma ita da katsina kam ba yanzu ba wadancan yaran ma don Haj tace ba zan Raba ta da su ba Amma da tun can sunyi Sallama Amma tunda Haj tace haka Suma su zauna kafin Naga Abinda ya kamata ayi gudunmuwar da Zaki bani kenan ki Taya ni Saka ido don na San Zaki iya.

Ta sauke AJIYAR ZUCIYA tana fadin. “To Allah ya kyauta in Sha Allah kuwa zanyi Abinda kace dama dai fita ce Kuma ta San baka bari sai dai wayar ce nake ga kamar ba zan iya Hanawa ba.

“In dai ba Haj zata Kira ba to kar ki Bata don na San Sameer zata Kira Idan Kuma Kina ga ba Zaki iya fada Mata haka ba kice ni na Hana ki Bata wayar tazo wuri na ta karbi tawa ta Kira ta.

Washegari kuwa Farida Bata fito ba tana d’aki nade Abun Duniya ya ishe ta Babu Abinda take so irin ta samu wayar da zata Kira Sameer Amma ta Rasa don haka ta tashi tana Jin haushin duk Yan gidan . Su Saddam da Hanan kuwa suna wurin Anty lubna cikin Yara suna ta wasan su don haka Taki fitowa har sai da Anty lubna taga shiru Bata fito ba ta Aiko Kiran ta Amma Bata je ba sai da ta iso da kanta inda ta same ta ta kirne fuska ko gaisuwa Bata samu ba.

Anty lubna ta kamo ta tana fadin
“Haba kanwata ban San ki da Duhun Kai haka ba. In anyi Miki Wani Abu ki fada min mana ? Kin San fa Baki da lafiya daure kizo kici abinci ki k’arasa shanye magungunan ki saura na yau kawai Yi Hak’uri kanwa ta giwa a gidan Mr Sameer.

<< Tana Kasa Tana Dabo 2Tana Kasa Tana Dabo 7 >>

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
2
Free daily stories remaining!
×