Labuda ta iso Gidan yayar tata wacce tace tazo tana son Ganin ta yanzu .
Basma ta fito da takardar manubar da take Shirin Yi ta Rattaba Hannun shaidu ta na nunawa Labuda.
"Kinga wannan takardar?
Basma ta fada tana Duban Labuda wacce ta zuba Mata ido tana sauraren Abinda zata ce.
"Ranar Sha takwas ga wata zamu koma kotu Ina so idan munje kice kina daga Cikin shaidun da Abdullahi ya bawa su Najwa gidan shi don an Soma zalunta ta ana bawa shegun Ya'yan Farida kudin jirgin da Abdullahi ya biya musu wai tunda kyauta ce sun ci. . .