Basma da ta ga Haj ta fita sabgar ta ana ta Shirin Auren Labuda kanwar ta da tsohon mijin ta Abdullahi Bata dauka Al Amarin na gaske bane sai da taga an saukewa Labuda akwatunan lefe seti Biyu yayin da Haj Baraka sai SHIGA da fita take don hattama kayan hidimar ta.
Basma ta Kira Labuda ta iso d'akin ta tana Duban ta kafin tace Mata
"Wai ke Kin yarda da Abinda Haj take nufin Yi da ke Naga Baki ce komai ba bare kiyi boren ba Kya son shi ko Kuwa dama munafunci ne kina son Abdullahi har. . .