Rana Ta Goma Sha Daya
A wannan ranar Wazirai suka fito da sassafe suka sa mutanensu suka shiga birni suna kiran mutane su taru a tsakiyar gari inda za a rataye Kabir. Mutane suka cika ana ta turmutsutsu har ba masaka tsinke, kowa na son ganin wanda ya ci amanar Sarki alhali ya amince masa. Daga nan Wazirai suka wuce gidan Sarki, kowanensu ya yi ado kamar ranar Idi. Suka faɗi gabansa suka ce, "Allah ya ba ka nasara, jama'ar gari gaba ki ɗaya sun hallara domin shaida hukuncin kisa a kan wannan yaro mai tsaurin. . .