Rana Ta Shida
Yayin da rana ta shida ta zo, fada ta cika, Wazirai duk suka hallara. Tun cikin dare suka zauna suka tattauna tsakaninsu kan yadda za su samu nasarar shawo kan Sarki Shamsuddin ya kashe yaron nan kowa ya huta. Don haka sai uku daga cikinsu suka gurfana gaba ɗayansu a gaban Sarki suka ce, "mu dai mun san ka ɗauke mu aiki, musamman domin mu ba ka shawara ta gari, kuma a kan haka muke. Muna mamakin yadda kake kawar da kai daga wanda ya ratsa tumbinka, ya keta mutuncinka, ya nemi shiga inda. . .