Mama ce ta daka masa tsawa tana lafiyarka kuwa Affan?
Yayi saurin katse kiran yana sosa kai hadi da saita kansa yace" Babu komai Mama" ya kama hanyar waje dan karta jefo masa tambayar da baida ansarta.
Duban sa ita kuwa maman tayi da alamun tambaya Amma ta share domin indai Affan baida rufi zaizo ya zazzage mata cikinsa.
Haka kwanaki suka cigaba shudewa har tsawan sati biyu Mami da Iya harma da Safna da har yanzu mijinta baizo ba suka maida hankali wajan kula da Widad da abunda yake cikinta.
Bangaran Shuraim ma haka shi da Affan Sosai suke. . .