Umar na tsaye yana kalle kalle ta fito riƙe da Muhd, yana hangota ya saki fuska itama daurewa tayi ta ɗan murmusa kamin ta ƙarasa ta gaidashi.
Cikin sakin fuska ya amsa gami da cewa sai kuma kika ganni ko, murmushi ta yi, “Eh wallahi.”
Shiru suka ɗanyi kamin ya ce, “Eh to daman batun Faruk ne.” Sai da gabanta ya faɗi jin sunan Faruk ta daure bata ce komai ba.
“Ɗazu ya zo ya samen ya faɗan komai da ya faru, banji daɗi ba sai dai abu ɗaya yamin daɗi.”
Ɗagowa ta yi ta. . .