Koda Ummu suka dawo Aisha ta riga ta tashi, harma ta yi shirin islamiya ta magariba dan haka kawai cewa Ummu tai Basira tazo tace Abbansu yace ta cewa Faruk ya ɗan jira su.
To kawai Ummu tace ta hau warkajamin ta.
******
Zaune take tana bawa Muhammad Mama, Hajiya ta fito ya dan tago kansa ya yaɗa mata hannu yana murmushi, Hajita tace ohni Rakiya, wato Ummu kindai ƙi yaye yaron nan, kinajin abinda Umman Walid tace miki ki yaye shi ba sai bikin yazo ba kinƙi yaro yai wayo.
Murmushi Ummu ta yi, fadin haka da Hajiya. . .