Ko da rana Ummu Hani bata rasa abin bawa ƙannen nata ba, dan maƙota nata kawo abin sadaka har baƙi masu zuwa gaisuwa ta samu na basu.
Kwana biyun duk a tsorace tayi su, yadda da rana gidan da mutane irin masu zuwa gaisuwa, sai dai dare na yi da kowa ya watse zata nemi nutsuwarta ta rasa, musamman in lokacin rufe gida yayi taje rufe ƙofa, sosai take kuka dan a lokacin mutuwar iyayan nasu sabuwa take dawo mata.
Zaune take tana yiwa Muhammad wanka, tun tana gogeshi da tsumma hartai ƙundun balar fara yi masa wanka. . .
This story make me so happy cuz sunana ne ummahani kuma bantaba ganin Anyi labari da sun anan bah Shiyasa abin yabani citta Allah yakara basira
Allah sarki fatan zaki cigaba da biyar labarin har karshe