LITTAFI NA BIYU
Shirun da Umman ta ce in yi shi din na yi na ja bakina na tsuke na zuba ido ina kallo tare da sauraron abin mamakin dake afkuwa.
Gabadaya yadda na yi zaton Baba zai yi hadin auren nashi ba haka ya yi ba.
Na jinjina al'amarin amma cikin zuciyata tun da ban isa in furta komai ba, Umma ta ce inja bakina inyi gum sai dai hakan ba yana nufin har zuciyata ma za'a tilasta mata yin gum din ba ne don haka ita kam tana ta faman kai kawonta.
Aure zai a hada. . .