A falon Umma na same ta zaune kan sallayarta na durkusa a gefenta duk da tsoron da nake ji na kar ta sake marina. Na ce mata, 'Umma Baba ya tafi." Ta gyada kai nuna alamar ta sani. Hawaye suka zubo shar! Daga idanuna loakcin da na buda baki na ce mata, 'Saboda ni ya yi fushi da ke?" Ta dan saki fuskarta ta shafa fatiha ta miko hannu tana share mini hawaye a hankali ta ce, "Ba saboda ke ba ne Adawiyya laifi na yi mishi."
Na sake kallon Umma cikin nutsuwa a kuma a tsorace na ce mata. . .