Umma tana jin haka ta fice daga ciki, shi kuma ya shigo, "Ke yarinyar nan kina so ki raina ni fa kwanan nan in kinra ki ki ce ba za ki zo ba?"
Na ce, 'A'a to mene ne in na fadi haka kai da kake murnar za ka samu matar da za ta raba ka da yan'uwa duka? Ai har da haka zai kara sawa in kwana, don in gayawa baba komai da komai, in yana da abin yi tun wuri ya yi."
Yaya Almu ya zuba mini ido ya ce, "Ke ki ce za ki zauna. . .