Skip to content
Part 18 of 49 in the Series Wace Ce Ni? by Hafsat C. Sodangi

Yaya Zubairu ya yi maza ya ce mata, “A’a Adawiyya ba ta yi mata komai ba, Umma ke dai kawai ki yi hakuri.”

“Ba komai.” Umma ta ce da shi.

Da daddare rannan ina kwance a bayan Umma ita ta ce in zo in hau bayanta in kwanta. Ina kwance a bayan nata tana tambayata.

“Jikinki dumi Adawiyya ko ba kya jin dadi ne?” Na ce mata na yi kwance cikin ruwa mai zafi ne Umma.

A hankali ta soma yi mini hira cikin nutsuwa, “Sai kin zama jaruma kin zama mai hakuri kan zaman da za ki yi da Babangida, shi kam ba ki da matsala da shi, don kuwa babu wani wanda zai so ki kwatankwacin son da Babangida yake yi miki. To amma, yan’uwanshi su ne matsala.”

Na ce mata, “Umma.”

“Mene ne?”

“Kin yarda in tambaye ki wani abu?”

“Uh, uh kar ki tambayeni komai yanzu barci ya kamata mu yi.”

Na ce mata, “To.” Na kara matsawa jikinta na jingina kaina da bayanta. Sannan na shiga barci.

Dare ya yi nisa lokacin da na ji Umma tana kiran sunana cikin salati da tsoro ta.

“Adawiyya! Adawiyya!!.” Na bude idona a hankali ina kallonta cikin rawar jiki a dalilin tsananin zazzabin da ke kadani kar! kar!! Kar!!! Na zuba mata ido ina kallonta cikin yanayin rashin lafiya. A hankali na bude baki na ce mata, “Ki yi hakuri Umma dazu na ji tsoron gaya miki ne su Anti Basira sun cijeni da karf.”

Umma ta ce, “Cizo?”

Ta shiga salati tana kuka. Yayin da take yaye ruhuwar tawa, don ganin inda cizon yake. Nan da nan ta shiga kuka mai tsanani tana cewa,

“Ya ya zan yi da ke Adawiyya? Ya ya zan yi da wadannan mutane da suke shirm tosa mini ke a gaba? Ba ki kuma yi musu komai ba, laifina ne kawai ya shafe ki, kiyayyar da suke yi mini ne za su dawo da ita kan ki.”

Ta sa hannu ta dauki wayarta. Yaya Junaidu ta kira. Har cikin dakin Umma ya shiga, ta nuna mishi jikin nawa, ya ce, ‘A’a wannan al’amari Umma hakuri fa za ki yi kawai tun da dai an kusa rabuwa ba kuma zai yiwu ki ce za ki yi wa yara wani abu ba, tun da dukkansu ya’yanki ne.”

Ta ce, “Haka ne.”

Cikin daren jiya Junaidu da Umma suka kai ni asibiti aka yi mini allurai, suka dawo da ni. Kwana biyu ina jinyar cizon da su Aina’u suka y1 mini, amma ba wanda ya sani, don yaya Junaidu ya ce kar a gayawa kowa, a yi shiru kawai.

Rannan yaya Almu ya kirani, na same shi a dakinsu. Ina shiga na Tsugunna ina sauraron shi ya kalleni cikin nutsuwa ya ce mini,

Rabi kina sanin saura kwana nawa ne bakinmu kuwa?”

Na zuba mishi 1do ina kallon shi, na ce, To  mene ne?”

“Ban taba ji kin ce mini komai ba.”

Na kalle shi na ce mishi, “Ni yanzu ai ba biki ne a gabana ba, muhimmin abu a wurina shi ne in san asalina, in san waye mahaifina. Sannan ma ni yanzu auren naka baya gabaná, don na gane matsala zai zamo mini mai girma, saboda haka na ce zan ga  Baba in roke shi in ya zo daurin auren ni ya baiwa Yaya Junaidu kai ya ba ka Rahama ko kuma..”

Da sauri Yaya Almu ya shiga cewa, “Ba ki da kai Rabi, ke ba ki da hankali, to in baki sani ba ma yau in gaya miki ke da Junaidu babu aure a tsakaninku.”

Na yi turus ina kallon Yaya Almu, yayin da shi kuma ya riga ya fusata da jin cewar zan bukaci a canza mini shi. Na ce mishi, “Yaya Almu…

Bana so kar ki gaya mini komai, je ki ki bukaci Baba ya canja miki ni, ni ba na bukatar canji a kan ki ke nake so, ba kuma zan bukaci a canza mini ke ba. Ni tun kina ‘yar jaririyar ki na ke son ki ban kuma taba dainawa ba. Je ki ki bukaci canji a kaina, in ba ki yi haka ba ai ba zan gane irin kiyayyar da kike yi mini ba.”

Na soma yi mishi kuka, saboda ganin irin fadan da yake ta yi mini. Na ce, Kana sona tun ina yar mitsitsiya, amma kake rerawa Aina’u wakoki a gabana? Ko ba ina nan a gidan nan ba kuke musayar Wasiku a tsakanin ku? Ko ban sha ganin wasikunta a dakin nan ba? Ba ka sha jaddada mini irin son da kake yi mata ba? Don me ba zan nemi canji a kan ka ba?

Shi na taba jin shi yana ambaton sunan wata budurwa ne? Kai ne kake son Aina’u kake son Uwale, na ga abin da Aina’u ta yi mini a kan sonka da take yi, ita ma ‘yar uwata kenan saura Uwale, ita kunma ban san wanda za ta yi mini ba, in mun gamu.

Cikin nutsuwa ya soma yi mini magana,

“In kin ji ina yi wa wata maka Rabi tsokánarki kawai nake yi, don in lura da kishinki a kaina, ba zan yi miki musun kina ganin wasikunta anan ba, amma zan yi miki musu idan kika ce kin taba ganin wasikuna a dakin ku. Maganar Uwale kuwa ba ni da wata Uwalen da ta wuce ki Rabi, ni ke ce Uwalena in kin yarda da wannan bayani da na yi miki to ina so ki kwantar da hankalinki ki toshe kunnenki ki daina sauraron duk wani zance da wani zai gaya miki kina nufin in ni zan rude ki Umma ma za ta rude ki? Har Baba ma ya yi miki hakan?

Na yi maza na ce mishi, ‘A’a.

“To ji ki ki shirya maza ki zo mu fita ki yi mini rakiya.”

Na yi shiru kawai na mike na fita. Na zo na samu Umma zaune a falonta na zauna nima kusa da ita na kalleta na dan yi murmushi, don ta san a cikin kwanciyar hankali nake. Ta sake kallona cikin nutşuwa ta ce, ‘Mene ne Adawiyya?

Na ce, ‘Ba komai Umma so dai kawai nake yi in tambaye ki ni waye ma ya haifi Yaya Junaidu?

Babu wata damuwa ta ce mini, “A’a yau kuma ba ki san uban Junaidu ba?”

Na ce, “Eh Umma gani nake kamar ba hakan ba ne mantawa na yi.”

To Alhajin Tudu ne wan Alhaji, wanda suke uwa daya, uba daya amma akwai mace a tsakaninsu ita ce yaya Lami, mahaifiyar Aina’u. Wannan dogon bayanin da na jaddada miki ya gamsar da ke?”

Na ce mata, “Eh Umma.”

Na dan sake kallonta na ce mata, “To nima Baban Tudun ne ya haife ni? Ta girgiza kai nuna alamar a’a. Ta sake kallona cikin murmushi tare da sansanyar ajiyar zuciya. Sannan ta sake kallona cikin nutsu wa ta ce, “In Alhajin Tudu ne ya haife ki da wani wanda ya isa ya ce ke ba ‘ya ba ce a gidan nan?”

Nan da nan na ga kuma eh haka ne. Na sake kallonta na ce, “To Umma gaya mini abu daya ni ‘yar ki ce?” Ta yi maza ta ce mini,

“Kwarai da gaske.”

Na sake cewa, “Ke kika haife ni?”. Ta zuba mini ido cikin nutsuwa ta ce,

“Kina tantamar hakan ne?”

Na ce mata, ‘A’a. To amma Umma…”

Ta ce mini, “Ke nake sauraro.”

Na ce,”Nuna mini nankarwar ki.”

Ta yi maza ta ce, ‘Yanzu kuwa.”

Ta sa hannu ta kwaye shimin da ke jikinta. Gasu nan rada-rada, kwance a kasan cikinta, har zuwa gefen cinyoyinta. Cikin zuciyata na ce tabbas wannan nankarwar da kan samu ne ta dalili haihuwar da ba ta halittar ba, Dadi ya kamani cikin zuciya na tabbata Ummana ita ce ta haifen. Na kalleta na yi murmushi na ce,

Umma.”

Ta tayani murmushin ta ce, ‘Mene ne Adawiyyah?”

“Ni tun da dai ke kika haifen to magana ta kare komai ma zai biyo baya to ina ganin shi din mai sauki ne, zan iya hakuri in aka ce ba Baba ne ya haifen ba, amma ba zan iya yin hakurin akan ki ba.”

Umma ta sa hannu ta jawo ni jikinta, na kwantar da kaina a gefen kafadarta cikin murya mai sanyi na ce mata, Ina jin mamakin abubuwa da suke fitowa kwanan nan a kaina Umma, na yi iyakacin tunanina na kasa gano dalili a ce wai aure ya haramta tsakanina da yaya Junaidu, ya kuma halarta tsakanina da yaya Almu. Wannan ba abin mamaki ba ne?”

Ta yi maza ta bata rai ta ce, ‘Eh abin mamaki ne sai ki je ki.yi ta bincike kina jiwo abin mamaki iri-iri.”

Na ce, Ba bincike ba ne Umma…”

Ta ce, To wannan magana ta ishen haka.”

“To Umma.” Na ja bakina na yi shiru.

Shirin biki na sosai da sosai Umma ke yi. In tsaya kwatanta lamarin ma bata lokaci ne, a kowanne lokaci cikin biki take, a kowane lokaci kuma a kan fita take, saboda al’amuran da ta ke gudanarwa ita da kawayenta guda biyu wadanda suke sune na hannun damarta, suka tafi Dubai, don sayayyar kayan dakin amare, wato Hajiya Hauwa da kuma Hajiya Furera.

Ina kwance ni kadai a dakinta, saboda tafiyar tasu sai na ji kadaici ya dame ni na tashi na jawo suwaita na dora kan doguwar rigar da ke jikina na fito waje ina tafiya ni kadai nufina in isa wurin baba maigadi in zauna in taya shi hira, sai na hango yaya Junaidu yana tsaye jikin kofar motarshi da ke bude hankalinshi kuma ya tafi wajen kallon wani abin da ke zaune cikin motar. Da sauri na nufi wurin nashi, don ganin mene ne? Ina isa wurin na gaishe shi ya dago kai ya kalle ni cikin murmushi ya ce da ni,

“Adawiyyah kin fito ne?” Na ce mishi, “Eh.”

To kun gaisa da Rahama ne?”

Lokacin ne na lura ashe ita ce a cikin motar ita yake yi wa wannan karkacewar da na ganshi yana yi.

Daga inda nake tsaye na ce mata, Sannu Anti Rahma.” Ta amsa cikin wata irin muryar da ban taba sanin tana da ita ba. A zuciyata na ce a’a har yaya Junaidu da aka girma a gabanshi sai,an yi mai wannan kashe muryar? Na dan yi murmushi, Yaya Junaidu ya kalleni ya taya ni murmushin ya ce, ‘Ai yan matan dukansu tuni suka watstsake suka shiga hidimar bakin su in da za ki leka dakin baki yanzu da za ki samu Aina’u da Basira suma samarinsu sun zo. Kabiru da Rashida kuwa tun safe suka bar gidan nan, Mustapha ne shi kadai ga shi can a bayan motarshi yana zaune ko za ki je mishi hira ne?”

Na yi kamar in ce mishi to, sai kuma na ji ina Son komawa wurin mu. Na ce mishi, ‘A’a Yaya Junaidu.” Na yi ma Anti Rahma sai da safe na juya na koma wurinmu. Ina shiga sashin Umma na ji jikina ya bani an shigo wurin. Na ja na tsaya ina kallon kofar falonta da ke rufe kamar Yadda na bar shi. Shiga sashin Ummana ba komai ba ne, don wuri ne na mutane ko tana nan ko ba ta nan. To amma wannan karon sai na ji kamar ba irin shigar da aka saba yi ba ne. Ina cikin wannan tsayuwar na hangi inuwar wani ta bayan dakinta. Da gudu na fita ina ihun barawo!

Barawo!! Da iyakacin karfina.

Gaba daya samarin gidan manya da yara dama duk wani wanda yake cikin gidan aka firfito. Yaya Almu ya bai wa Baba maigadi umarnin rufe get kar a bar kowa ya shiga ko ya fita.

“Barawo ki ka ce Adawiyya?” Yaya, Junaidu ya tambayan jikina yana bari na ce mishi, “Eh a sashin Umma na gan shi.”

Shi da Yaya Almu da yaya Harnza suka taso ni a gaba saura kuma suka ce su tsaya a nan, don kar wani ya ce zai zo ya fita, tun da katangar gidanmu dai babu mai iya tsallake ta. Muka isa sashin Umma na ja na tsaya daga nesa na nuna musu ta inda na hango inuwar suka je suka duba suka dawo, suka ce babu kowa.

“Anya ba tsorata kawai kika yi ba Adawiyyah?”

Yaya Almu ya ce, “An shigo ga alamar kafa a nan,”

Gaba daya suka sake zubawa wurin ido. A hankali suka rinka bin takun suna dubc-dube zuwa can yaya Junaidu ya ce, Zo nan Mustapha ba a yi wani abu a wurin nan ba? Da sauri ni da yaya Hamza muka karasa wurin na su, yaya Almu ya kalli Hamza ya ce mishi, “Yi gudu ka kira mallam tare da Baba maigadi, su Musa kuma su tsaya a get kar su bar kowa ya fita ko waye shi”

Su Baba maigadi da maiam suka iso.

‘Malam ba a yi tono a wurin nan ba?” Yaya Almu ya tambaye shi. Ya ce, Eh to da alama dai kam an yi.”

Baba maigadi ya ce, Eh to ai da akwai baki a gidan shekaran jiya kun tafi kai Hajiyá airport su kuma aka shigo da su.”

Yaya Junaidu ya kalle shi ya ce, ‘Amma shi ne ka yi shiru ba ka fada ba’?” Ya kara rage murya ya ce, ‘Ai na gane an saba kawo irin su, su gama, kwanakinsu su fita, ita kuma Hajiya nan ba mai yarda a rinka kawo mata irin wadannan laburan ba ne.”

Yaya Almu ya nemo shebur ya shiga kwashe kasar wurin. Tuno sosai aka yi aka tarar da wata katuwar kwarya. Yana daga kwaryar sai ga dan kunkuru mai rai a kife. Gaba daya wuri ya dauki salati. Ni kam kuka na kama yi. Ya sa hannu ya dauko dan kunkurun wanda ni tsoro ya hanai kare mishi kallo,  balle in ga abin da ake cewa an rataya mishi.

Malam ya karbi dan kunkuru shi da Baba maigadi suka tafi bayan sun jaddada muhimmancin a yi shiru kar a tada maganar.

Yaya Junaidu ya kalleni ya ce, “Mu je can ki kwana a wurin mu. Ita ma baba Talatun da take tayaki kwana ta kwana a wurin su kawai a rufe nan din.”

Na ce mishi, “To.”

A dakin su Yaya Almu ina kan katifarsu su kuwa hirarsu suke yi a kan kujera. Farkawa kawai na  yi cikin dare na ga ni kadai ce a dakin, amma ban tsorata ba don gaba daya wannan sashin nan samari ne. Ina  kwance idona biyu ina tunanín abin da ya faru sashin Umma.

“Yau me ake nufi da wannan abin da aka yi? A kashe ta ko a yi mata me? Aurena da yaya Almu ne kawai ya jawo hakan ko kuwa dama can ana yi sani ne kawai ban yi ba?”

Hawaye suka suka yi ta zubowa a idona, saboda tausayinta da ya kamani, abin da na sani shi neU mma zaune take zuciya daya da kowa, amma kuma ita ake zargi wai mai magani ce ta mallake baba, sai yanda ta yi da shi. Ina cikin haka na ji kamar ana magana a waje. Da sauri na tashi na sanya suwaitar da hular sanyina na fita.

<< Wace Ce Ni? 17Wace Ce Ni? 19 >>

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
2
Free daily stories remaining!
×