Rannan muna kwance ni da ita a gado dama kuma tare muke kwanciya ita kuwa yaya Balki tana daya gadon sai naji tamfar Uwa tayi magana na ce mata me kike fadi? Sai da nayi mata tambayar sau biyu sai ta ce bada ke ba ne nace da waye? Ta ce da wannan ne na sake jin wani faduwar gaban nayi maza na mike zaune na ce mata a ina kika ganshi Uwa? Kan ta ce min komai sai yaya Balki ta ce min ke kuwa me yasa kike irin wannan binciken ne Zuwaira? Me za ki iya yi ne. . .