Skip to content
Part 6 of 30 in the Series Tambaya by Haiman Raees

Wane Irin Uba Ne Ni?

Amshi:

Wane irin uba ne ni? 

Wai ni wane irin uba ne ni? 

Wane irin uba ne ni? 

Wai ni wane irin uba ne ni? 

01.

Jama’a ku saurara, zan yo batu babu ja-in-ja

Zuciya ce ta ruɗe ni, gashi yau na taɓo danja

Ina son ɗiyata ce, kun ga na ko jawo jarfa

Riga ta gaza hana aikin banza, wa ke batun ma jamfa.

02.

Ɗiyata da na haifa, ita zuciyata take ƙauna

Tsantsar nuradinta, yasa na kira ta sanyin raina

Gashi nan fa ta girma, komai dai masha Allah

Ga ɗiyar akwai ladabi, halayyarta sai madalla.

03.

Na kori dukkan samarinta, don bani so su yi min cikas 

So nake da na sam dama, in tsinci haja a ɓagas 

Bani so kowa ya raɓeta, don ni kaɗai ke muradinta 

Ko aike ban so a tura ta, don bani so tai ta ragaita. 

04.

Na zamo tamkar kare, ɗiyata nake ta farauta 

Kullum ina tunaninta, na manta ni na haife ta 

Tunani a har kullum, yaya zan same ta

Burina a har kullum, idanu sui ta kallonta. 

05.

Hancina a koyaushe, so yake ya ji ƙamshinta 

Na sha in ta mafarki, wai ina tare da ita 

Na riga fa nai nisa, banjin kira ku bar mini mita 

Shaiɗan ya min huɗuba, kan lallai na nemeta. 

06.

Tunda har ta kira ni Uba, dole ne in umurce ta 

In ce ta ɗan duba, ta taimaki Abbanta 

In ta so ta min tababa, wai kawai sai na shaƙeta 

Haka shaiɗan yai ta riya min, zuciya har fa ta aminta. 

07 

Watarana ina ɗakina, kawai na kirawo ta 

Dama a loton nan, na aiki babarta 

Na ce ta je can ƙauye, don ta dubo iyayenta  

Ita ɗiyata na ce ta zauna, akwai makaranta. 

08.

Na riga fa na shirya, tabbas yau zan same ta 

Ta shigo ɗakina, sai na ce ta sakki jikinta 

Kafin ta ma zauna, na riga fa na sa sakata 

Na kulle ƙofar gam, babu hanya bare mafita. 

09.

Da ta nuna tababa, ai nan da nan sai na shaƙeta 

Ashe na taɓo Nepa, akwai aljanu a kayinta 

Aljanin da ya tashi, ji kake titim sai duka 

Kafin ka ce mene, tuni har na fara yin kuka. 

10. 

Jikina ya yi talata, domin ko na sha duka 

Ina yin shesheka, neman afuwa ina kuka 

Ina ta faman ihu, neman agaji na maƙwafta 

An shigo cetona, ƙofar ko na sa sakata. 

11.

Kafin a ɓalle ma, tuni na riga na fa jigata 

A taƙaice dai malam, da ƙyar aka ƙwace ni 

A sa’ilin nan ma, jikina duk rauni 

Ko’ina sai tabbai, sai assibiti aka kaini. 

12.

A loton ga na farka, na ji ni ina gurnani 

Zufa tana karyo min, kamar a kogi aka tsamo ni 

Takaici nan ya sarƙeni, na zauna ina ta tunani 

Ashe mafarki na yi, damuwa ta aure ni. 

12.

Allahu na tuba, Allah ka yafe ni 

Sharri na sheɗani, Allah ka kare ni 

Tunani ma mai muni, Allah ka kiyaye ni 

Ruɗi na zamani, Ya Rabbana ka kare ni. 

13.

Ka shirye ni shiryawa, daga duk baɗala ta zamani 

Ko da ina kogi, ko bayan na haye tsauni 

Albarkacin Manzo, shugaban masu imani

Na tuba na bika, Ya tabaraka Mannani. 

Bookmark
ClosePlease login

No account yet? Register

Rate the story.

Average: 5 / 5. Rating: 2

As you found it interesting...

Follow us to see more!

<< Tambaya 5Tambaya 7 >>

2 thoughts on “Tambaya 6”

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.