Bayan sun gama cin abinci su ka zauna su ka d'an ta'ba hira sannan su Ahmad suka mi'ke domin za su je gidan su Al-amin domin su fad'a wa inna halin da ake ciki, ko za ta zo ta kwana awajen ta, fita sukayi su ka bar su khadijan, bayan fitan su khadija tace wa Maimuna ta taimaka mata tayi sallah, taimaka mata ta yi don har yanzu ba 'karfi a jikin ta, tayo alwala, maimuna ta shimfid'a mata d'ankwalin ta don ba Dadduma. A zaune ta samu tayi sallolin da ake binta. . .