Tunda daga ranar da na bar gidan, shikenan komai nasu yayi sanyi, ANTY bata cika fitowa ba ko da yaushe tana cikin ɗ’akin ta a ƙwance, gaba ɗaya damuwa tayi mata yawa, kullum tunanin halin da nake ciki takeyi, Daddah tayi faɗan har ta gaji amma shiru babu sauyi…
Tabbas bari na gida tamkar rushewar wani reshe ne na gidan, MAN bai taɓa sanin san da yake min ya kai har haka ba, kullum bai da aiki sai tunani na komai yake baby! duk abinda yake duba sai baby! koyar wa ma ta gagare shi duk dan sabida dani! yafi kowa shiga damuwa a cikin gidan, abinci ma yana cine kawai amma bawai dan yana me dadi ba, gashi har yanzu Mommy bata dawo ba, ta wuce wajen daddy din su tare da Auta, Daddah ita kaɗ’ai ce take kula dasu, ku san kullum sai MAN ya aika da saƙon shi gidan mu, kuma ana cin sa’a Kawu ne yake amsa, kalamai na bege da tsananin ƙewa ta da suke, kafin sati biyu ta cikika KAWU ya amshi wasiƙun sa sun kai tallatin, gashi ya gagara gane takamai-mai din wanda da yake aikowa,
Kalmar da yake gani shine (A&M)…
Batun ƙawa ta kuwa mun haɗ’u da ita, mun ɗaura a inda muka tsaya, sosai take bani labarin abinda ya faru bayan bana nan, wani nayi mamaki wani kuma na shiga damuwa, tunda na dawo gida aka sauya min makaranta me tsada nake zuwa…
Ƙwance nake yau bana jin zuwa ko ina, tunanin na tafi me zurfin gaske na jima a haka sosai, cikin hukuncin Allah tamkar a mafarki na ringa tuno rayuwar gayun da nayi, da irin mutane da nayi ma’amula dasu, matar da na gani a ranar dana farka ta faɗo min irin kukan da take, tabbas yanzu na gane dalilin rashin sakewa ta a cikin gidan nan, har da ƙewar su dake nuƙur-ƙusata ta a ɓangare guda, lallai nayi ƙewar su ba dan kaɗai ba, take wasu siraran hawaye suka zubo min, cikin taushin murya nace” ina ƙewar ku sosai ANTY NA!!, dama zan sake ganin ku ko sau ɗaya na!…”
A lokacin da nake wanna tunanin itama haka ne ya kasance a wajen, ANTY picture dinna take kallo cike da ƙ’auna ta, cikin siririyar murya tace” nayi ƙewarki sosai ƴata, Allah yasa kina tunawa dani dear…”
Daddah dake shirin shigowa tayi saurin koma da baya, tausayin yaran ta na cika mata zuciya, yanzu nan ta dawo daga bangaren MAN dake cike da begena, Ashe nan din ma duk abin ɗ’aya ne…
Tun daga ranar dana fara tunanin su komai nawa ya sauya, walwala ta ragu ko makaranta naje ina gindin bishi, duk irin yanda nake da nacin karatun abun ya dawo sai a hankali, tun malaman suna ƙoƙ’ari har suka fara gayawa Kawu na halin da ake ciki…
Ya sha kamani ina kuka, a ɗaki na amma dana ganshi sai na wayance, na fara kame-kame, cikin dabara KAWU na ya fara ajiye min letter da MAN yake aiko min da ita, ɗaya bayan ɗ’aya, kullum sai na tsinci ɗaya a kan merro dinna, tun ina shiga damuwa har na saba….
A hankali yanayi kalaman sa masu sanyi daɗɗaɗ’a zuciya sukayi mutuƙar tasiri a ƙoƙon raina, har nake ji in bashi ba sai rijiya, yanda ake gaya rubuta kalaman daki-daki sune suka masifar ratsa ni, kullum da kalar wace nake karantawa, soyayyar sa tayi min mugun kamo duk da har yanzu ban san ko waye shi ba, *na faɗa makauniyar soyayya* me tsananin hatsari da sarƙ’aƙiya….
A hankali Kawu na ya fahimci halin dana faɗa, sai ya janye ƙwana biyu baya ajiye min, tabbas na shiga matsanancin tashin hankali, lokacin da na fahimci an daina aiko min da saƙo, nayi kuka tamkar Raina zai fita…
Yau kimanin ƙ’wana uku kenan banga saƙon JARRIME NA ba sunan dana raɗa mai kenan…
Babu inda ban bincike ba a cikin ɗaki na, inayi Ina kuka cikin mutuƙar begen sa na fara fitar da sauti me taɓa zuciya, cikin murya me hauhauwa nake cewa” haba JARRIME NA! me yasa zaka wahalar da zuciyar da ta jima a cikin baigen ka, shin baka tunanin wanne irin hali zan shiga in banci karo da saƙon ka me ratsa min jini da tsoka ba, tabbas na san tawa da ƙare tunda na riga da faɗo tarƙon makauniyar soyayya me wahalar sha’ani, wai me yasa ma bazaka baiyyana min kai ba, haƙiƙa Ina mutuƙar san ka da ƙaunar, kalaman ka sun gama makanta min zuciya da jijiya, nayi imani da Allah da mazan tsira muddin ka baiyya min kai ka ko a yaya ka ke zan kasance dakai har ƙarshen numfashi na… cikin kuka nayi maganar…
Kawu na dake tsaye cikin taga, wani irin tausayi na ya kama shi, cikin sauri ya sakar min takadar dake hannun sa, kafin na ankara ya fice a gidan..
To yau kam MAN ya kai maƙura domin ya gaji da aika saƙo shiru har yanzu babu amsa, dan haka yau yayi shiri na musamma domin zuwa da kan shi…
Allah sarki abin tausayi, sai da ya gama rubuta abinda zai furta mata insun haɗu yau, sannan kimtsa kan sa cikin mutuntawa ya nufo gidan su kai tsaye…
_amincin Allah ya tabba ta a gareki ya haske idaniya ta, ki sani cewa soyayyar ki da ƙaunar ki yana neman zautar dani, ina miki wani irin so wanda na gagara fahimtar sa, wallahi tallahi zan iya sadaukar da farin ciki na, nutsuwa ta , walwala ta, an’nuri na, rayuwa ta, muddin zaki k’asance a cikin farin ciki, tabbas ni kadai nake ƙ’aunar ki, Ina miki san so, SAHIBA TA ki dawo gare mu ko hankalin mu zai ƙwanta, ki tuna damu ko maji dadi a cikin zuciyar mu ko da sauya ɗ’aya nee, ANTY NA tana mutuƙar bukatar ki haka nima I LOVE SO MUCH BABY!!!…”””_
Ina gama karantawa na mike da sauri ina waigege ko zanga wanda ya shigo har cikin gidan mu ya ajiye min wanna saƙon, kai tsaye waje na nufa domin na ganewa idanuna…
A dai-dai lokacin kuma ya faka da motar sa, cikin wata rantsatsiyar shi, ta alfarma gaskiya ya haɗ’u iya haɗ’uwa, kamar yand kuka san shi cikin yauki din nan nasa da izza haɗe da takama ya fito yana karema fuskar gidan namu kallo tamkar bai taɓ’a zuwa ba kallo ɗaya za kayi mai kasan tsananin raini ne yasa shi yin wannan kallon…
Ya gama shirin sa tsaff ya fito zai wuce, ya nemeni motar da ya niyyar hawa ya rasa, cikin bakin rai Haidar ya raɗawa me wanke musu motaci kira, jikin sa na rawa ya karaso inda yake, ko kallon sa baiyi ba sabida takaici yace” Ina da motar dana ce ka wanke min kafin na fito yanzu?..”
Cikin risinawa yace” yallaɓ’e Alhaji ƙarami ya fita da ita yanzu…” cikin rashin fahimta yace” waye shi!?..” “Alhaji ANNUWAR!…”
A hankali Dadda ta ɗago ta zuwa jikin ta, cikin nutsuwa tace” shitt!! ya isa haka!!..”
Ƙare musu kallo nayi tass, sannan ‘na kalle Kawu na, haɗi da sakar mai tausasan murmushi, a hankali nace” ina san ka sanyin idaniyata!..”
Shi ma martanin murmushi ya mayar min, daga bisa ni yace” Hajiya ‘in babu damuwa ina son magana dake?..”
” BISMILLAH!..” cewar Daddah.. Waje suka fita ni kuma aka barni da jama’a ta har yanzu MAN bai waigo ba, tunda na kalle ANNUWAR sau ɗaya ban sake gigin kallon sa ba, hankali na gaba d’aya yana wajen Hajiya Nusaiba, da take ta ƙoƙari ganin na tuna su…
(Kun dai san manta komai nata tayi, ba wai haukacewa tayi ba, duk abinda kayi mata zata iya rikewa, haka zata iya tunawa ko da memory dinta ya samu lafiya, musamma ita tunda tana da kayefin tunanin, zata na ganine tamkar a mafarki tayi wata rayuwar daban…)
Cikin gajiyawa nace” Kiyi haƙuri Hajiya, nima yau na fara ganin ku!..”
Maganar ce ta daki zuciyar ANTY cikin sauri tayi baya, MAN yayi saurin tare ta, haushi ya kama ANNUWAR…
” HAJIYA zan so na bar muku ita a hannun ku, ni kai na sai zuciyata sai tafi nutsuwa da hakan, amma ina jin tsoro sosai da yanayi da take ciki, ki ƙwantar musu da hankali insha Allah nan ba da jimawa ba zan dawo muku da ita, zanyi ƙoƙari sosai na ganin bata manta da ku ba, kuyi haƙ’uri dan Allah ku bar min ita nima na samu nutsuwa, zata dawo muku cikin sauki…”
Kallo mutuntawa Hajiya Daddah tayi masa cikin jin dadi da tausayi sa tace” haƙiƙa naji dadi furicin ka sosai, Allah ya saka da alhairi, amma abinda nake so da kai shine, karka taƙura kan ka abinda bakayi niyya ba, na san yanda kake ƙaunar ƴarka, ita ma tana ƙ’aunar mahaifin ta, muna san muga MUNIBBAT a cikin farin ciki, me ɗaurewa kullum ƙwanan duniya addu’ar da muke mata kenan, Allah ya amsa kuma mun gode masa, duk cikin mu babu wanda zai so ya raba ta da abinda take so, a yanzu babu wanda tafi ƙaunar gani da san zama dashi sama da kai! kana tunanin zamu so wannan farin cikin nata ya rushe? a’a baza mu zama masu san kan mu ba gaskiya, zan so ka bar ta a wajen ka duk lokacin da ta bukaci ganin mu, insha Allah zata gan mu, kamar yanda muke kula da ita a wajen mu, baza mu canza ba insha Allah mun gode sosai Allah ya bar zumuci, ka ci gaba da riƙe amana tabbas zakaga ribar hakan, Allah ya tsare gaba mun gode…”
Jikin sa yayi mutukar yin sanyi, ko magana ma ya gagara…
Har yanzu ban ga fuskar mal Haidar ba, a haka ya fice da Anty tana kallo na hawaye na bin kuncin ta, ANNUWAR na bin bayan su, a waje suka tarar da Daddah daga nan su kayi sallama da Kawu suka fice a asibitin gaba ɗaya…
Gaskiya na yarda ni ƴar gata ce a wajen Kawu na, duk inda na motsa sai ya tambaye lafiya ta, abun gwanin ban sha’awa zuwa dare aka sallame mu muka dawo gida, babu wanda baiyi mamaki ba gani a gyara gidan fas dashi, musamma ɗaki na a zuba mun wasa manya kayan ɗaki masu bala’in kyau da tsari, tamkar ba gidan mu ba, gaskiya ana ƙawata abun sosai, dadi ya kamani sai tsalle nake ina murna, cikin jin dadi nace” Kawu duk wannan nawa ne ni kaɗ’ai?..”
Shima murmushi ƙarfin hali yayi min haɗi da cewa” eh mana yar gidan Kawu, duk dan kiyi farin ciki ne ai…”
Ko da na bude cikin siff din kaya ne masu yawan gaske da tsada, komai ana zuba min a ciki ina can ina shirme na na jin dadi, Kawu na ya ɗauki wata farar takarda da aka ɗ’anne ta da ƙwalin wata danƙ’areriyar waya, bai bari na gani ba yayi saurin ficewa a ɗ’akin…
To kamar yanda aka saka min wannan kayan a ɗaki na, haka ma ɗakin matar Kawu na ya kasance, amma fa bai kai nawa kyau ba gaskiya, sai murna take ganin ta samu gani ma…
Can zaure ya tsaya, sosai ya fahimci me ake nufi da saƙon, ya jima sosai yana tunanin aciki su waye yayi wannan aikin, amma ya kasa fahimta, a ƙ’arshe rubutun ana rubuta (A&M) me ya hakan yake nufi to? iya tunanin sa yayi amma ya gaza ganewa dole ya haƙuri ya dawo cikin gida jikin sa a sanyaye…
Kimanin sati biyu kenan yanzu da dawo ta cikin ahali na, bana fuskar wata damuwa a ko wanne ɓangare, rayuwa ta nake kamar yanda na faro ta tun farko, har yanzu Kawu na bai koma wajen aikin sa, gashi kusan kullum yana bani labarin rayuwar da nayi a wani gida, da irin soyayyar da ake min, amma fa har yau baice min ni bace, abinda yake ɗaure min kai ma shine a duk lokacin da muka zaune hira dashi, da ya fara bani labari naji ya faɗ’i abinda babu shi, zance ba haka bane kaza ne, na kayi mamaki ina zauna ni kaɗai na fara tuna rayuwar da nayi a baya, sai nake gani tamkar mafarki nakeyi…
======>
Tunda daga ranar da na bar gidan, shikenan komai nasu yayi sanyi, ANTY bata cika fitowa ba ko da yaushe tana cikin ɗ’akin ta a ƙwance, gaba ɗaya damuwa tayi mata yawa, kullum tunanin halin da nake ciki takeyi, Daddah tayi faɗan har ta gaji amma shiru babu sauyi…
Tabbas bari na gida tamkar rushewar wani reshe ne na gidan, MAN bai taɓa sanin san da yake min ya kai har haka ba, kullum bai da aiki sai tunani na komai yake baby! duk abinda yake duba sai baby! koyar wa ma ta gagare shi duk dan sabida dani! yafi kowa shiga damuwa a cikin gidan, abinci ma yana cine kawai amma bawai dan yana me dadi ba, gashi har yanzu Mommy bata dawo ba, ta wuce wajen daddy din su tare da Auta, Daddah ita kaɗ’ai ce take kula dasu, ku san kullum sai MAN ya aika da saƙon shi gidan mu, kuma ana cin sa’a Kawu ne yake amsa, kalamai na bege da tsananin ƙewa ta da suke, kafin sati biyu ta cikika KAWU ya amshi wasiƙun sa sun kai tallatin, gashi ya gagara gane takamai-mai din wanda da yake aikowa,
Kalmar da yake gani shine (A&M)…
Batun ƙawa ta kuwa mun haɗ’u da ita, mun ɗaura a inda muka tsaya, sosai take bani labarin abinda ya faru bayan bana nan, wani nayi mamaki wani kuma na shiga damuwa, tunda na dawo gida aka sauya min makaranta me tsada nake zuwa…
Ƙwance nake yau bana jin zuwa ko ina, tunanin na tafi me zurfin gaske na jima a haka sosai, cikin hukuncin Allah tamkar a mafarki na ringa tuno rayuwar gayun da nayi, da irin mutane da nayi ma’amula dasu, matar da na gani a ranar dana farka ta faɗo min irin kukan da take, tabbas yanzu na gane dalilin rashin sakewa ta a cikin gidan nan, har da ƙewar su dake nuƙur-ƙusata ta a ɓangare guda, lallai nayi ƙewar su ba dan kaɗai ba, take wasu siraran hawaye suka zubo min, cikin taushin murya nace” ina ƙewar ku sosai ANTY NA!!, dama zan sake ganin ku ko sau ɗaya na!…”
A lokacin da nake wanna tunanin itama haka ne ya kasance a wajen, ANTY picture dinna take kallo cike da ƙ’auna ta, cikin siririyar murya tace” nayi ƙewarki sosai ƴata, Allah yasa kina tunawa dani dear…”
Daddah dake shirin shigowa tayi saurin koma da baya, tausayin yaran ta na cika mata zuciya, yanzu nan ta dawo daga bangaren MAN dake cike da begena, Ashe nan din ma duk abin ɗ’aya ne…