Juyo dani tayi cike da jin haushi na, ta wanke min fuska da mari, tana hawaye take cewa" kina hauka ne MUNI? kin san me kike cewa kuwa? MAN fa! buluci zakiyi musu? shine fa wanda yayi jinyarki a lokacin da baki san inda kan ki yake ba, shine wanda yayi sadaukarwar jinin sa har kika samu damar ci gaba da rayuwa! wannan shine sakayyar da zakiyi masa kenan? shine mutumin da yaso ki a lokacin da baki da wata nutsuwa! ya so ki tsakani da Allah! ya ƙauna ce ki, shine JARRIME da kikewa kuka a ko wanne. . .