*****
Kimanin wata biyu kenan shiru Mommy bata sake maganar aure ba, yanzu ko da yaushe tana d'aki abinta, magana bata dame ta ba...
Allah sarki Daddah ita ko wannan saban halin da Mommy ta fito dashi sai duk ta bi ta damu kan ta, kullum cikin leka ta take ta gani ko lafiya, sabuwa ladama ke damun Mommy tunnani take ta ina zata gyara k'usk'ure ta musamma a wajen surukar ta me ladabi, tunda ku san kullum sai na kira ta a waya na gaidata, tun tana kin dauka har ta fara wani lokaci tai shiru. . .