Nnamdi Azikiwe International airport, Abuja.
Hanam da Haris ne tsaye a jikin wasu kujeru, yayinda Masarrat, Salwa, Al'amin da kuma Khalil wanda ke riƙe da Arya suke tsaye daga kusa da su suma.
Yau sati biyu kenan da rasuwar Abba, dan haka Masarrat tace su yau zasu koma, kuma tare da Arya zasu tafi, dan Hanam ɗin ta yayeshi, kuma su Al'amin ne suka riƙa mata magiya kan ta bari su tafi da shi, babu yanda za ta yi haka ta amince musu, ita fa tunda Abba ya rasuma jifa-jifa take ganinsa, rabonta da ta. . .