Ta shiga motar yana mata kalan tuhuma.
Shikuwa Abubakar ganin haka ya tashi Shima yayi hanyar dawowa Hulwa tunda yasan suma nan zasu taho.
Har ta shige suka fara tafiya Uncle Mujahid baice komai ba.
Sai da suka kusan zuwa gidan ya dubeta yace" Shahida" ta dago tana kalan sa.
Yace" wan can yaran da na gani gurinki yazo?" .
Ta gir-giza kai yace" amma me zakiyi a gurinsa ?"
Tace" daman -daman kawai gaisawa zamuyi".
"Gaiswa" ya maimaita tambayar yana dubanta .
Yace" Shahida buɗe kunan ki da kyau kijini zan fada miki wani abu".
Yace " babuke babu wani namiji. . .