Skip to content
Part 19 of 30 in the Series Yar Karuwa by Harira Salihu Isah

Suhail yana dariya ya ce, “Yaya ACM wato ainahin Allah sa Mom ta ji ka, mu dai ba ruwan mu, Mom muka sani kuma muna bayanta, Aunty Amarya kuma mun bar mata kai.”

Bunayd murmushi kawai yayi ya miƙe, tare da fadin, “je ka shirya mu fita.”

Suhail ɗakinsa ya wuce ya wasta ruwa ya shirya cikin ƙananan kaya, Suhail ma fa ba ƙaramin kyakkyawan saurayi ba ne, saboda yan da kuɗi da jin daɗi suka zauna musu, idan ka gansa ba za ka ce twin’s brothern Suhaila bane, musamman da yake namiji, shekarunsu 17 amma idan ka kallesa za ka ɗauka ya kai 25 saboda gaɓa.

ACM Bunayd ma ɗakinsa ya wuce, cikin ƙasaita kaman wani Sarki haka ya rage kayan jikinsa ya rage daga shi sai short, tatoo na jikinsa yake kallo yana ɓata fiska, kiston kan nasa ma sai da ya gama masa yastine-yastine sannan ya shige banɗaki, bai wani jima ba ya fito ɗaure da guntun towel a ƙugunsa, sharp-sharp ya shirya, pencil Jean’s ya saka da t-shirt mai shegen kyau, Bunayd fa ƙarshene a kyau fan’s, dan ko (DMD jinin indiyawaa albarka).

Suhail ya gama shirinsa, ya jima da sauƙowa palourn amma Bunayd bai fito ba tukunna, zama Suhail yayi yana danna haɗaɗɗiyar wayansa, har dai sassan jikinsa mai isar da saƙon ƙamshi zuwa ƙwaƙwalwansa, ta sanar masa da isowan yayan nasa, saboda ƙamshin Bunayd ma na daban ne, indai ka ji sau ɗaya, to idan ka kuma ji sai ka sheda shi ɗin ne.

Ɗagowa Suhail yayi tare da yin murmushi, cikin harshen turanci ya ce, “wow! Yaya kayi shegen masifaffen kyau da haɗuwa, dole ma wata babe ta ƙyasa idan mun fita.”

ACM Bunayd hannunsa ya zura cikin aljihunsa, yayi gaba bai ce wa Suhail komai ba.

Da sauri Suhail ya miƙe, shi ma cikin takunsa na ƴan gayu ya bi bayan yayan nasa, da ya ke Suhail ya iya mota, to sai Bunayd ya dakatar da driver, suka shiga su biyu Suhail ya ja su.

Suna tafiya Suhail na kawo masa hira yana amsawa, nishaɗi suke abinsu kaman abokanaye, Suhail ne ya ce, “Yaya ACM ina muka nufa?”

Bunayd kiston kansa ya taɓa yana ɓata fiska, ganin haka Suhail ya gane abin da yake nufi, dariya kawai Suhail ɗin yayi dan rigiman yayan nasu na basa dariya, mutum sai gayu da rigima kaman mace, dan haka wajan da ake masa kiston sa na ƴan gayu suka nufa, Suhail na faɗin, “Yaya ka rage gayu fa akwai mutuwa atou, duk kiston ma yaushe ka yi sa”, ya faɗa yana dariya.

ACM Bunayd hararan ƙanin nasa yayi, tare da buɗe marfin motan ya fice, dan sun iso wajan kiston.

Sun jima sosai a wajan sannan aka gama komai, ba ƙaramin kyau kiston kuma ya yi wa Bunayd ba dan an sauya style nasa, yanda kasan kaman wanda ya fito daga wata ƙasar daban, daga wajan kuma suka shiga gari ya ƙamshin dahuwa, su ne basu koma ba sai cikin dare bayan sun je wajajan shaƙatawa, dan Bunayd ba’a raba sa da maganan club.

Bunayd sai da yayi sati guda a Turkish ya gama duba ayyukansa, sannan ya kuma biyo jirginsa ya koma Lagos, sai da ya bi gidansa yayi abinda zai yi, sannan ya wuce gidan General.

Ɓangaren Abeed da Amaryansa Nusaiba soyayya suke shumfiɗawa mai tsafta, cikin yarda da juna da kuma haƙuri da juna, dan yanzu ƙafansa ya warke rass, yau ma kaman kullum yana kwance a ɗaya daga cikin kujerun haɗaɗɗen palourn su, iyaka short ne kawai a jikinsa yana danna wayansa.

Nusaiba kuma tana kitchen tana girki, tana sanye da legis da half vest mai shegen kyau da hulanta, ta gama girka komai sannan ta fito tana shagwaɓe fiska, tun da Abeed ya ga fitowanta a kitchen, da yanayin yacce tayi da fiskanta sai ya fara murmushi, ita kuma cunna baki tayi.

Abeed na danne dariyansa ya miƙa mata hannu, da nufin ta zo wajansa, tana shwagaɓa ta ƙaraso tare da shigewa jikinsa, murmushi yayi tare da shafa bayanta ya ce, “Ai sai da na ce kibari babyloff, amma kika dage ke sai kin yi girki, kuma dai ni ban ce dan girki na auro ki ba.”

Nusaiba cikin shagwaɓa ta ce, “Uhmn! To idan ban yi ba me za ka ci, ko haka za ka zauna da yunwa?”

Abeed ido guda ya kashe mata tare da cewa, “Ina da abinda zan ci ne da ya wuce ke babyloff, ai indai da honeypot to bana yunwa, ni yanzu ma fatan kin gama aikin naki ki bani abin daɗi.”

Cikin wasa Nusaiba ta bugi ƙirjinsa ta ce, “Kai fa my captain ka cika uhmm…uhmñ…”

Abeed dariya yayi ishashshe ya ce, “Ai gwanda na cika uhmm.. uhmm, jaraba da takura ba, to gwanda nayi a bani abuna da kyau, yanzu kin ga na warke komawa zan yi aiki, sannan idan na jefa ƙwallo a raga, baby ya zo yana shakara ai dole na dinga ɗaga ƙafa.”

Tura baki tayi ta kwantar da kan ta a faffaɗan ƙirjinsa ta ce, “Ni dai ƙafata ƙafar mijina, dan tukunyar zuma ta riga ta saba, ba za ta iya suvirving ba idan ba uhmm, wannan”, ta faɗa tana ɗaura hannunta akan Dragon da ya jima da fara huci.

Wani irin lumshe ido Abeed yayi, yana jin ta riga da ta gama kunnasa, lasan kunnenta yake yana faɗin, “Me sunan shi uhmn ɗin, sarkin kunya da yin yaren kurame.”

Murmushi tayi tare da ɗago kanta, a kunnensa ta masa raɗa, wan da ni dai Uwar batoorl kunnena bai jiyo mini ba atou, shi kuwa Captain Abeed murmushi yayi tare da kashe mata ido yana faɗin, “Ashe dai wiffeyn tawa ma A ce, irin wannan babban suna haka ko sakayawa babu, ina laifin a ce masa Dragon ɗin.”

Nusaiba jikin Abeed ta shige tana dariyanta, nan kuma wasan ya sauya aƙala, daga dariya ta buge da stoste masa nipples nasa, wan da ya kusa saka Abeed sumewa, nan fa suka fara haukata junansu da zafafan hidiman soyayya da ƙauna, a hankali ya raba ta da kayan jikinta duka, kwantar da ita yayi ya fara bin sassan jikinta da lasa, lokacin da ya isa Palace kuwa Nusaiba ƴar ƙaramar hauka ta yi, nan ta dinga sambatu tana ihunta na daɗi, wan da ke ƙara ingiza Abeed, a sannu a hankali yayi nisto cikin honeypot nata, kusan a tare suka sauƙe ajiyan zuciya.

Hidima Abeed ya din ga yi, yana shagalinsa, daɗi sai haukatasu yake, har suka samu nustuwa, inda ya ƙanƙame babyloff tasa kaman zai mayar da ita ciki, ba tare da ya zare jikinsa a nata ba, yake kallon cikin idon ta, tura baki Nusaiba ta yi shi kuma ya kashe mata ido guda.

Abeed bai ƙyale Nusaiba ba sai da yayi second round, suka samu nistuwa duka ya ɗagata kaman ‘yar baby, shi ya musu wanka sannan suka tsarkake jikinsu, towel ya ɗaura a ƙugunsa, ita kuma tayi ɗaurin ƙirji, palourn suka dawo ta kawo musu abinci, saving nasa tayi, za ta zuba nata sai ya riƙe hannunta yana bin ta da wani mayen kallo, a plate guda suka ci abinsu, shi yayi feeding nata, har suka ƙoshi, shi da kansa ya tattara wajan sannan ya dawo ya zauna ya kunna musu kallo.

Nusaiba miƙewa tayi ta nufi hanyan ɗaki, Abeed da kallo ya bi ta ya ce, “sisss! Ƴammata minti biyu.”

Juyowa tayi tana murmushi ta ce, “Yes!”

“Sai ina? Za ki kaste mini ƙarfin da nake ƙarawa idanuwa na.”

Murmushi tayi ta ce, “kaya zan saka Captain.”

Ɓata fiska Abeed yayi, wai bai yarda ba, shi haka yake son ya dinga kallonta, ƙallonsa yana ƙara ƙarfi, dan dole ta haƙura ta dawo ta zauna a cinyansa suna kallo cikin soyayya, Abeed sai taɓe-taɓe yake.

Lokacin komawansa nayi kuwa ya tattara babyloff tasa suka yi Adamawa land of beauty, a barrack suka zauna, kusan kullum yana maƙale da Nusaibarsa, har dai yayi nasaran saka ƙwallo a raga, ta fara laulayi kuma.

Bunayd zaune a palourn General, shi da Momsee da kuma General ɗin, Momsee girgiza kai tayi ta ce, “wai dama da gaske kake lefen za ka yi wa yaya na auren da zai ƙara?”

General kallon Momsee yayi ya ce, “To me a ciki, yaro yana goyon bayan raya sunnan ma’aiki SAW, Allah maka albarka my man, Allah ƙara maka buɗi, nima idan na tashi ƙarawa sai ka haɗa ma tawa ma.”

Bunayd haɗaɗɗen kistonsa ya shafa ya ce, “General ni ba ruwana kada ka haɗa ni da Momsee na.”

Murmushi Momsee tayi, bata ce komai ba, kawai ta cigaba da abin da take yi, Bunayd ya ce, “Momsee to in miki transfer ne ko kuma a nemi currency na ƙasan da za ki je a baki?”

Hararansa Momsee tayi ta ce, “ka je da kanka ni ba zan je ba na fasa zuwa.”

General dariya yayi ya ce, “haba first lady ta Sufyan, kin fasa kam, ya kike so ayi idan na tashi yin nawa auren?”

Momsee ƙara haɗa fiska ta yi irin tana kishin nan, General kuwa ya samu gangara abinsa sai zolayanta yake, Bunayd sai ƙunshe dariyansa yake, dan rigiman iyayen nasa dariya yake basa, General da Momsee masoya ne na haƙiƙa, ji yake dole ma ya je Kano dan ya ga ita kuma Mom ya za ta yi, ko halin ko in kulan nata har da akan kishi.

Sai da aka koma rarrashi, sannan Momsee ta amince, suka gama magana komai da komai, next week za ta tafi ta haɗo kayan.

Wani sati na zuwa, Momsee ta shirya tafiya Dubai, General ma cewa yayi zai rakata, nan suka kama hanya su biyunsu, ACM Bunayd sai dariya kawai yake, yana faɗin sabon honeymoon kawai General zai je yi da wayo, ba rakiya ba.

Alhaji Mukhtar ma a nasa ɓangaren shirinsa ya fara, duk da ba su yanke lokaci ba, amma ɗauki da soyayyan Ramlatunsa ya ƙi barinsa ya sarara, shiri kawai yake yi, a sama ita ma za ta zauna, dan daman saman ne part nasa da Mom, ƙasa na yaran ne.

*****

Mami ba ƙaramin gyara kan ta take ba, yanzu tunaninta ɗaya ne kawai zuwa biyu.

Na farko ta amince za ta yi aure saboda Allah da kuma farincikin gudan jininta, amma yanzu tunani take na kamata yayi a haɗa auren da na Banafsha ko kuma a riga yin nata kamun na Banafsha, idan aka riga yin nata to Alhaji zai yi komai na wakilci kaman shi ne mahaifin Banafsha, amma kuma kamun a ce lokaci yayi na aurenta, ai zaman agolanci za ta yi, kuma tana gudun a samu mastala daga wajan matar Alhaji ta zo ta dinga muzgunawa Banafsha, dan ita bata yarda da zama in da za’a muzgunawa yarinyarta ba, idan kuma aka ce a haɗa auren nan ma ba mafita ba ce, sabo da hidiman sam-sam ba zai haɗu ba, musamman ga iyayen Aliyu, idan ba sa’a ba za’a samu akasi ma.

Gaba-ɗaya kan Mami ya ɗau Chaji, daga ƙarshe kawai addu’a tayi na Allah ya tabbatar da alkairi a lokacin da yake dai-dai, sai ci-gaba tayi da gwangwaje kan ta.

An shiga court da case na Umma, angabatar da duk abin da ya kamata, Umma ta amshi laifinta, Mami ma tayi magana akan ta yafe, sai dai alƙali ya ɗaga sauraran ƙaran, sai wani zaman kamun a yanke hukunci, gaba-ɗaya su yaya babba damuwa ta cika su, basu san irin hukuncin da za’a yankewa mahaifiyarsu ba, ga kuma sunan matarsa Hindatu da za’a yi saura kwana biyu, gaba-ɗaya ya koma sai a hankali.

Duk abin nan da ake yi kuwa Abbaa ko a jikinsa, dan ko ƙofa ta kashi na court ɗin ma bai je shi ba, kuma ba zai je ba, dan Umma Sabeera ta jima da sane masa a rai, Ummu ma dai lamarin ba wai ya mata daɗi ba ne, kawai ba yan da aka iya ne, sai dai du’ae.

Yau Saturday da yake jajiberin sunan matar babban yaya, da wuri Umaima ta shigo wajena da wani ledan ƴan gayu a hannunta, samun mu tayi ni da Mamina muna zaune a palour, gaishe da Mami tayi ta amsa tana murmushi, ta ce, “Gwoggonun yarinya har kun gama naku shirin kenan.”

Murmushi Umaima tayi ta ce, “Eh Maminmu, yanzu ma kayan da za mu saka na kawo mata.”

Hararanta nayi na ce, “kaya dai, bayan wanda muka amso a wajen tailor.”

Ledan ƴan gayu ta mika mini ta ce, “Ni dai ga naki, saƙo maƙoƙo na isar.”

Ƙin amsa nayi na ce, “Wato ma saƙo ne, to shikkenan ai ki maida banaso, ina da nawa ya isheni.”

Wani kallo Mamina ta jefeni da shi, wanda ya sanya ni tura baki, miƙa hannu nayi na amsa ina hararan Umaima, ita kuma sai maste dariyanta take tana mini gwalo, ina amsa na haɗa fiska kaman wacce aka kawo wa saƙon mutuwa.

Mami girgiza kai tayi ta ce, “Umaima ki ce an gode ko, Allah masa albarka ya ƙara buɗi.”

Da “Ameen”, Umaima ta amsa, tare da miƙewa tana dariya ta yi wa Mami sai da safe ta fice abinta, dan ko kulata naƙi yi, haushinta nake ji kaman ita ce ta turo kayan.

Ina ture-turen bakina kawai naji Mami ta sake mini ranƙwashi, “Auch! Wayyo Kai naaa!”, na faɗa har da ƴar ƙwalla na, sai da na gama sosa wajan, sannan na kwantar da kai na a cinyan Mami na ce, “Mami me na yi ni kuma, Uhmn! To ki yi haƙuri.”

Kunnena Mami ta kuma ja, ta ce, “Au! Tambaya kike me kika yi ko, dan ban ƙara miki ba, Banafsha sam-sam bakya ji, bansan halin wa kika ɗauko ba wallahi, ni babu wani nawa da yake da irin mugun halin nan, to Allah ya shirya mini ke, kuma saura idan kin tashi tafiya kibar kayan a nan, za ki ga yanda zan yi da ke a gidan nan.”

Tura baki nayi, kawai na bawa Mami haƙuri, har sai da ta haƙura, sannan na tashi da kai na, buɗe ledan nayi, wani Arnen haɗaɗɗen swiz-less ne, da mayafinsa, da takalminsa, da sarƙansa mai abin hannu da zobe, ga jaka.

Mami tana murmushi ta ce, “Wow! Masha Allah! Allah ƙara masa buɗi, Allah sa a kashe lafiya, kaya yayi kyau sosai, inyee wa ya ga gudalliyan Maminta da leshin Amare.”

Duk da kayan ya mini kyau, amma bana jin zan saka su, a ɓoye na ja guntun tsaki dan kar Mami ta ji ni, murmushin yaƙe kawai nayi nima na ce yayi kyau, tattare kayakin nayi na kai ɗaki na cusa a Sip na, ko damuwa da na gwada su ban yi ba.

Palourn na koma muka ci-gaba da hira da Mamina, har lokacin ya ɗan ja, sannan kowa ya wuce ɗakinsa ya kwanta.

Washe-gari kuwa da sassafe Mami ta tashe ni, aiki na taya ta na haɗaɗɗen abincin ƴan gayu, sai da ta gama duka ta saka a babban kula, sannan ta fito da carton’s na abun sha, muna gama shirya komai ta sanya ni naje na yi wanka, ina shigewa ɗakina sai ga Umaima ta shigo da nata kayakin a hannu, gaishe da Mami tayi ta bi bayana.

Mami wayanta ta ɗaga ta ƙira layin yaya Sadeeq yaron Ummu, yana zuwa suka gaisa cikin mutuntawa, sannan ta nuna masa abincin, fita yayi suka shigo da abokanansa suka ɗauka, suka wuce wajan raɗin suna da abincin.

Ni da Umaima wanka muka yi, muka shirya cikin kayan mu, riga kaman kimono da pencin skirt, Abbaa ne ya ɗinka mana anko, ba ƙaramin kyau muka yi, ba.

An yi suna lafiya an gwangwaje, mai jego sun sha kyau da yarinyarta ZAINAB KABEER(Noor), muma gwaggonun yarinya ba’a bar mu a baya ba, har da Nana bealkysou duka anko muka yi.

Mamina ba ƙaramin hidiman abinci ta yi ba, wan da daga yaya babba har matarsa sai da suka ji daɗin hakan, duk da dai daga farko Mai jego ta so yi mini rashin kirki, amma daga baya ta yasar da makamanta, domin ko su a gidan ba su yi abinci mai daɗi na zamani irin wan da Mami tayi ba, dan ko da Abbaa da ya samu labari ba ƙaramin kukan zuci yayi ba, na rashin samun Mami a mastayin matarsa.

Ya Danish sai zuba ido yake ya ga ta inda zan ɓullo da kayan da ya turo mini, amma naƙi sakawa, ga shi Mami tana busy bata kula ba balle ta mini dole sai na saka, Umaima ta yi jabaranta da tijaranta ta gama, amma dai ban saka ba, wannan abu ba ƙaramin ciwo ya yiwa Ya Danish ba, musamman da na ga kayan jikinsa na san nufinsa anko ya mana, sai danne zuciya yayi kawai ya ɗau na Annabawa.

Haka aka yi bikin suna aka waste, Masha Allah kowa sai albarka yake sakawa Noor, dan yarinyar ta yi goshi, ga shi kama take da Umaima sosai, kuma Umaimatyna kyakkyawa ce, anyi bikin suna an shuɗe babu Umma Sabeera.

Sai dare bayan sallahn isha’i sannan sai ga sallaman Malam Abbo, Mami kallona tayi ta ce, “yauwa hidima ya sa na sha’afa ban sanar da ke da wuri ba, idan yayi ki faɗa masa zuwa ranan juma’a iyayensa za su iya zuwa dan mun yi magana da Alhaji.”

Kallon Mamina kawai nayi na jinjina kai babu musu, sai da ta shige ɗaki sannan na ɗan gyara ina cunna baki na fice, iso na masa ya shigo, bayan ya zauna na wuce na kawo masa abin mosta baki, sannan na samu waje na zauna, shi dai sai bi na yake da kallo, ɗan shagwaɓe fiska nayi na ce, “Barka da zuwa Malamina”, na faɗa tare da ɗan satan kallonsa, wato ba gaskiya Malam Abbo ya haɗu iya haɗuwa, ko wace iriyar kaya ya saka amsar sa suke kaman dan shi aka yi su.

Malam Abbo murmushi yayi tare da cewa, “Barka da tarbana Sayyadata.”

Rufe fiska nayi cikin jin kunya na gaishesa ya amsa, yana murmushi ya ce, “Ya kuma gajiyan hidima? Ina nawa rabon?”

Ina murmushi na ce, “Naka ai na daban ne Malamina, na tana de shi kuma yana ajiye saboda kai.”

Cikin nishaɗi muke hira da Malam Abbo, inda ba ya gajiya da baje mini sirrin zuciyarsa, duk da dai har yau ba wai ni na baje masa makamancin irin wannan sirrin bane, amma hakan bai damu Malam Abbo ba, shi dai burinsa ya mallakeni, kuma kaman kullum yau ma sai da yayi maganan yaushe zai turo magabatan sa.

Marairaicewa Malam Abbo yayi kaman mai shirin yin kuka, idanuwansa a kai na ya ce, “Sayyadata a taimaka mini, nasan ke ce baki ba da order ba tukunna, dan Umma kam mun jima da yin magana ta ba da nata, dan Allah a taimaki documents nawa ai mini signing, wannan contract ɗin yana buƙatan approval naki ranki ya daɗe shugabar duniyar zuciyata.”

Dariya na yi ɗan dai-dai, tare da sanya tafukan hannayena na kulle fiskana, a hankali na ce, “Wai..waii..Uhmn..wai ba..wai ka..tu.roo.”

Malam Abbo karkaɓe kunnensa yayi tare da juya mini su yana saurarena, cewa yayi, “rankishidaɗe ƙara faɗa na ji, na tabbatar ba labarin gizo da kullum kunnena ki bani bane.”

Ƙasa nayi da kai na, na ce, “Wai ranan juma’a, su abbanmu za su iya zuwa.”

Malam Abbo dan murna ji yake kaman ya rungume Banafsha, gaba-ɗaya farin ciki ya hanasa jimawa yau, da wuri ya mini sallama ya tafi, ni dai sai dariya kawai nake yi, ina mamaki kaman wan da aka basa kujeran Makka, wani abu ne ya faɗo mini a rai, a hankali na sauƙe ajiyan zuciya tare da faɗin, “Allah rufa mana asiri duniya da lahira, wato duk iya ɗaukin da namiji ke yi wajan ganin ya aure ki, da duk soyayyan nan, shi ne a watarana baya hana shi kuma ya buɗi baki ya ce, ya sake ki, to Allah kyauta.”

Bayan fitan Malam Abbo, naje na kulle mana ƙofan gida, sannan na dawo na wuce ɗakina a gajiye, wasta ruwa nayi tare da bin lafiyan gadona na kwanta, ko ɗakin Mami ban je ba, balle na mata sai da safe.

Washe-gari Litinin muka tafi College, dan yanzu mun fara test, kuma ba jimawa za’a fara exam’s ɗin ma.

Mun cinye wannan satin lafiya, ranan juma’a muna dawowa makaranta, tun da na ga Mota a ƙofan gidanmu, to ko ba’a faɗa ba nasan Alhaji ne ya zo, karo na farko da zuwansa ya mini daɗi, tun da nasan yanzu kam in Allah ya yarda nan da wasu satuka, zai zama mijin Mamina.

Shiga gidan nayi ɗauke da sallama a bakina, Alhaji kaɗai na gani zaune a palourn yana danna wayansa, ina murmushi na ƙarisa tare da stungunawa, kai na a ƙasa na gaishe sa, yana murmushi shi ma ya amsa ya ce, “sannunku da dawowa ƴar albarka.”

Amsawa nayi na tambayesa ya hanya, ya su Majeeder, jin ban mance sunanta ba, sai ya murmusa ya ce, “Duk suna lafiya tana gaisheki, wai yaushe zan kai mata ƙawarta.”

Murmushi kawai nayi na miƙe na shige ɗakina, bayan na masa a huta gajiya.

Ina shiga ɗakina na faɗa kan gado na cikin farin ciki, gani nake ma kaman gobe ne za’a ɗaura auren Mamina, wani abu ne ya faɗo mini a rai, wan da ya sa na ji ba daɗi, a hankali na furta, “Umaimatyna ba zan so yin nesa da ke ba, nasan ba zan taɓa samun ƙawa, Aminiya kuma ƴar uwa irinki ba”, a hankali na goge ƙwallan da ya zubo mini sannan na miƙe na rage kayan jikina, ruwa na wásta na saka kaya mara nauyi na jawo system na ina game abina.

Ɓangaren Malam Abbo tun a ranar yana barin wajan Banafsha, ya samu mahaifinsa da maganan ya samu mata a nema masa aurenta, Iman Adamu wan da suke ƙira da Abiy, ba tare da jan magana ba ya yi na’am da batun yaron nasa, domin Malam Abbo shi ne ɗan Auta a wajan iyayensa Imam Adamu (Abiy), da Malama Hauwa’u (Ummi), iyayensa da yayyunsa biyar duka suna ƙaunarsa, musamman yayyunsa mata da kuma Abiy.

Daman Abiy ya jima yana bin sa akan ya kawo mata yayi aure, amma Malam Abbo yana zillewa, ƙyalesa kawai Abiy ke yi dan shi ɗan so ne, kuma shi kaɗai ne ya rage ba su aurar ba, to yanzu jin wannan batun ba ƙaramin farantawa Abiy yayi ba, tun da ya san yaron nasu yana da ilimin addini da na zamani, kuma yana da nustuwa, ba zai zaɓowa kan sa matar da bata dace ba, dan haka amsawa yayi akan ranan juma’an za su je ba ɓata lokaci ma Insha Allahu.

Washe-gari Abiy ya yiwa Ummi maganan, ita ma ta yi addu’an Allah sanya alkairi, sannan aka sanar da yayyunsa duka mata da mazan, babban yayansa Ya Hussain shi Abiy ya aika ya ƙira masa baffanunsu.

Bayan baffanun sun zo Abiy ya sanar musu, su ɗin ma addu’an sanya alkairi suka yi, domin duk sun san tun da Abiy ya amshi batun, to ba wani mastala daga ɓangaren matar da Aliyu ke so ɗin.

Malam Abbo ya sanar da Banafsha akan iyayensa za su zo ranan juma’a, kuma da yamma, dan haka tuni Banafsha ta sanar da Mami, ita kuma ta sanar da Alhaji har ya ce ta faɗawa Abbaanmu ma dan a fita haƙƙinsa, tun da shi ma a ɗiya ya ɗauki Banafsha, dan haka duk kowa na cikin shiri.

Duk neman auren yayyun Aliyu da ake zuwa, Abiy ba ya zuwa ƙannensa ke zuwa, amma wannan karon tun da ɗan autansa ne, juma’a nayi ya shirya da shi za’a je, su Ya Hussain da baffanunsu sai zolayan Abiy suke, wai yana banbanci ya fi son Aliyu, shi dai murmusawa kawai yake yi, ya ce musu ai auren na daban ne shiyasa, ga Aliyu ga kuma faɗima, ai babban lamari ne, aure ne na manyan iyaye, dole ya je da kan sa, suna nishaɗinsu haka suka kamo hanyan gidan su Banafsha.

A ɓangaren su Alhaji kuwa, da farko kaman za su koma gidan Abbaa su tari baƙin, amma kuma sai suka zauna a gidan Mami tun da duk ɗaya ne, palourn ya sha gyara sai ƙamshi kawai ke tashi.

Mami sai da ta gama shirya delicious, sannan suka tafi gidan Abbaa ita da Banafsha.

Ko da su Abiy suka iso, babban yaya ne ya musu iso, cikin fara’a su Alhaji suka tarbesu, babban yaya ya je kitchen ya jido kayakin da Mami ta nuna masa akan na baƙin ne idan sun zo, jere musu yayi a gabansu.

Sai da suka gaggaisa, sannan suka taɓa abin da yaya babba ya jere musu a gabansu, bayan sun gama sannan suka fara magana cikin mutuntaka da girmama juna.

Duk abinda ya kamata sun magantu a kai, yarinya tana karatu kuma an amince za ta ci-gaba, Alhaji ya faɗa musu mahaifinta ya rasu amma dai su ne waliyanta, an gama tattauna komai an kuma stayar da biki wata biyu kacal, sannan duk abubuwan da suka kamata za’a yi su kamun bikin, amma sun biya kuɗin na gani ina so dubu ɗari.

Bayan sun gama magana suka sallami juna, su Alhaji har da raka su suka yi, Abiy suka koma cikin farin ciki da yaba karamci irin na iyayen matar da Aliyunsa zai aura, ko da suka bawa Ummi labari ita ma taji daɗi, kuma daman sun dawo da abun sha da sauran abubuwan da Mami ta yi, Ummi sai da ta turawa sauran yayyun Malam Abbo mata a gidajensu, su ma sun ji daɗi ƙaninsu ya samu ƴar gidan mutunci.

Abbaa tuni suka zama abokai da Alhaji duk da dai kowa na kishin ɗan uwansa, sai da suka magantu sannan Abbaa ya masa sallama ya koma gidansa, sannan Mami ta dawo, ita dai Banafsha tana can tare da Umaima suna ta yiwa juna stiya.

Mami ta shigo da sallama, ta samu Alhaji na tattare mata palourn, murmushi Mami tayi ta staya tana kallonsa, Alhaji dagewa yayi har da shara, abun sai ya bawa Mami dariya ta amsa tana faɗin, “rufa mini asiri Alhaji, shara dai da kanka.”

Alhaji ƙin bari yayi, dan dole Mami ta haƙura suka gyara wajan tare, sannan suka zauna, kuɗin ya ɗauka ya miƙa mata tare da faɗa mata duk yan da suka yi da iyayen Aliyun.

Mami wani irin wawan ajiyan zuciya ta sauƙe, danne abin da take ji tayi, cikin dauriya ta murmusa ta ce, “Alhaji kai ma ai mahaifinta ne yanzu, musamman da za ka auri mahaifiyarta, ka ajiye mana kuɗin a wajanka, hakan da kuka yi ma bakomai yayi, Allah ya nuna mana da rai da lafiya, tun da sun amince da maganan karatunta.”

Jinjina kai Alhaji yayi, tare da sakar wa masoyiyarsa Mami murmushi, na jin daɗin furucin da tayi, cewa yayi, “To yanzu na yarinyarmu nan da wata biyu idan Allah ya yarda, mu kuma fa sai nan da yaushe? Sati biyu ko ɗaya ma yayi ai ko?”, ya faɗa yana jifanta da kallon da ita kaɗai ta san fassaranshi.

Mami murmushi tayi ta ce, “Ah! Da sati ɗaya kam ai gwanda kawai a ce gobe.”

“Ai da na fi farin ciki ma idan ya kasance goben, kin ga ango nake tun yau ma”, Alhaji ya faɗa yana murmushi.

Mami ta murmusa ta ce, “Allah huci zuciyan Angon Ramla to, yanzu dai a bar shi yan da muka yi da farkon, a bar shi rana ɗaya da na Banafsha, idan ya so bayan sati guda sai na tare, kasan ba zai yiwu ayi tun yanzu na bar ta ita kaɗai a nan ba, idan muka tafi kuma zai iya yi wa iyayen mijinta nisa, bana son a samu wani mastala kuma.”

Jinjina kai Alhaji yayi ya ce, “Duk yan da kika ce haka za’a yi Amaryan Mukhtar, duk da dai ba’a so ba ƙanin miji ya fi miji kyau, amma maganan sai bayan sati ki tare ni ban yarda ba, ana wastewa a hidiman Banafsha, muma za mu yi namu hidiman, sannan yanzu ya za’a yi da batun zuwanki Makka ɗin?”

Mami ta ce, “shi ma dai a bari sai na aurar da yarinyata, dan a yanzu ba zan iya tafiya ko ina na bar ta ba, gwanda ma idan na kai ta gidan miji.”

Murmushi Alhaji yayi ya ce, “Yau da gobe duk ɗaya ne a wajan Allah, kuma ga mai nisan kwana, Allah nuna mana da rai da lafiya, Allah kuma ya tabbatar da alkairi, yanzu dai da yardan Allah nan da wata biyu nima Ango ne.”

Mami ta ce, “Ango na Ramla ba.”

Alhaji dan farin ciki hulansa ya cire ya mikawa Mami wai ya bata kyauta, saboda cewa da tayi Angon Ramla, Mami sai dariya take, haka suka dinga hiransu cikin nishaɗi.

Malam Abbo tun da Abiy ya faɗa masa yan da aka yanke, farinciki kaman ya kashe sa, wato da yardan Allah nan da wata biyu Sayyada Faɗima ta zama mallakinsa, ranan kwana yayi nafilan godiya ga Allah da ƙara neman alkairin wannan al’amari.

Abbaa ya taya Danish baƙin ciki sosai na rashin Banafsha, amma babu komai ai matar mutum kabarinsa ce, Allah ya basa ta gari wacce ta fi ta, dan haka sai ya yanke hukuncin ɗagawa Danish ƙafa, sai zuwa gaba kuma ya masa maganan aure, amma tun da an riga da an fara na Ya Farooq to in Allah ya yarda shi kam za’a yi.

Alhaji sai da yayi sati guda sannan ya tattara ya shirya komawa Kano, bayan sun yanke magana da Mami, ya faɗa mata ko stinke kada ta saya na maganan Banafsha, komai yayi alƙawarin mata, hatta da stinstiyan shara duk zai saya, abinda ya kama na kuɗi ma ta masa magana, Mami har rasa abin da za ta cewa Alhaji take, illa iyakaci ta ɗau aniyan zama da shi, cikin soyayya da ƙauna da kulawa da tarairaya da haƙuri da kuma Amana, cikin daɗi da rashinsa duk za ta jure ta yi haƙuri ta zauna da shi, saboda shi ne kawai halaccin da za ta masa ta saka masa, akan kyautatawan da yake mata, ita da gudan jininta.

Tun da aka yanke kwanakin auren, Mami ke stuma kan ta da ƴar ta, yanzu ko ina Banafsha za ta je sai da niƙab da Safa, Allah ya taimake ta a college ba’a yi magana akan sakawan ba.

Bayan wata guda suka fara exam’s, in da a tahfiz kuma suka dage da karatu maganan musabaƙan da za su yi a Abuja nan da wata biyu, kuma suna yi da sati guda za’a yayesu a tahfiz ɗin.

Umaima idan ka kalli bussyn da take yi tun yanzu ka ɗauka ita ce Amaryan, duk da karatu da suka mai da hankali akai arabi da boko, amma bai hana Umaima shirye-shirye ba.

Ɓangaren Umma an kuma sauraran ƙaranta, in da aka yanke mata hukuncin ɗaurin rai da rai, a hakan ma saboda Mami ta yafe mata shi yasa ba’a yi maganan tara da za ta biya ba, wannan hukuncin ba wanda ya yiwa daɗi, musamman yaran Umma, Umaima ta yi kuka kaman za ta kashe kanta, yaya babba da ya Mus’ab duk sun fawwalawa Allah, suna dai kan addu’an Allah sa haka shi ne sanadin shiryuwan mahaifiyarsu.

Ya Danish kam ba’a maganansa, tun da ya kasa kunne da kyau ya ji tabbacin aure Banafsha za ta yi, shikkenan ya yiwa Mubi ƙaura, musamman da Ummansa bata nan, Abbaa ya masa uzuri tun da yasan zafin ya haɗu masa biyu ne.

Sati biyu muka yi muka kammala exam’s namu, shikkenan kuma muka ajiye maganan zuwa college a gefe, tahfiz ɗin ma ba kullum nake zuwa ba, a rana sau ɗaya nake zuwa kuma sai yamma, yanzu da biki ya rage sati biyu Mami a cikin kuɗaɗen da Alhaji ya turo mata, ta ɗauko mana mai gyaran jiki, a nan Mubi matar take amma asalinta Kanuriya ce, ni da Mamina wani irin sihirtaccen kyau na musamman muka yi, kuma Alhaji tun da ya tafi bai kuma zuwa ba, sai dai su yi waya da Mami kawai, ni ma mun yi waya, duk abin da nake buƙata kuma ya tambayeni akan na faɗa masa, ni dai iyakaci na ce komai aka mini dai-dai ne Allah saka da alheri.

Malam Abbo ma shiri yake yi a nasa ɓangaren ba kama hannun yaro, gidan da za mu zauna da komai an gama gyarawa, sun kawo kuɗin goro, kayan aure ma sun haɗa, amma sai aure saura kwanaki za’a kawo, sadaki kuma sai ranan aure, Malam Abbo da yake ɗan gata ne, duk da shirin aure da yake yi amma ko rama bai yi ba, sai ma wani kumatu da ya ƙara da kyau, saboda suna da rufin asiri kuma kusan komai yayyunsa da iyayensa ke masa, zuwa yanzu kuma da ya rage sati biyu kwata-kwata baya samun zuwa wajena, kuma ko naje tahfiz ba wai magana muke da ya shafi bikinmu ba.

*****

Captain Abeed da Amaryansa soyayyansu suke sha, tare da renon cikinsu da yanzu yake wata uku, Abeed ririta ta yake tamkar ƙwai.

General da Momsee sai da suka yi wata guda mai kyau sannan suka dawo, kaya niƙi-niƙi, kayaki masu kyau da kuɗin gaske.

Da yake duk basu san wa Papi zai aura ba, to duk ɗaukansu ko budurwa ce, kayaki suka haɗo har da sanji Momsee ta dawo da shi, su Suhaila sai farinciki da murna kaman wani an ce kayan nasu ne, Allah-Allah suke lokacin biki yayi su tattara su tafi Kano.

ACM Bunayd ƙiran Papi yayi ya faɗa masa akan kaya sun zama ready yaushe za’a kai, amma Papi ya ce ya bari tukunna sai ya yi wa Amaryansa magana, Bunayd dariya ya dinga yi wai shikkenan Mom ta gama yawo, Amarya ta mallake Papi tun ba’a kawo ta ba, idan aka kawo ta kuma ai Mom ta koma ƴar kallo.

Akwatuna goma sha biyu ciff, ga kuma guda shida a gefe na Mom, dan Momsee ta ce basu isa ba sai an haɗowa Hajiya Sa’adatu na faɗan kishiya, ko da tana da nata kuɗin amma wannan ya kamata a mata, dan haka shirya kaya aka yi ana jiran maganan Papi, yana cewa Yes za’a sako su a jirgi a taho Kano da su.

Tun da aka saka rana Alhaji Mukhtar ya sanar da General Sufyan, maganan yan da auren zai kasance da komai, dan haka Momsee tuni suka fidda ankon su, idan an kawo Amarya ranan Monday washe-gari Tuesday za su yi walima, Wednesday kuma a yi family and friends, ɗaurin aure kuma su General duk za su je Mubin a ɗaura a can.

Duk shirin da Momsee ke yi wa su Ramla su Suhaila, to tana yi da Majeeder, dan tasan ba lallai Hajiya Sa’adatu ta saurari maganan shiri ba balle ta yi wani abu wa Majeeder, Bunayd kuma duk da haka ya turawa Majeeder kuɗi sabo da kisto da ƙunshi da sauransu, kuma Papi ma ya mata ɗinkuna da duk abin da ya kamata, dan haka Majeeder haɗaɗɗen gift ta saya, ta ajiyewa ƙawarta da za su zo tare da amaryan Papi.

Har biki saura wata Hajiya Sa’adatu bata da labari, ta ga dai Alhaji ya ƙara gyara ɗaya part ɗin a sama, bata dai ce masa komai ba, har biki ya rage saura sati biyu, ya saka aka kawo wasu ranstastun haɗaɗɗun furniture’s, sai da ya gama shirya komai, sannan ya tura mata kuɗi masu yawan gaske.

Hajiya Sa’adatu ganin abin na Alhaji ya ƙi ci, kuma ya ƙi cinyewa, ta riga ta gama shirin kwanciyanta dan a gajiye take jiya ta dawo da ƙasar waje akan issuen business nata, kuɗin da Alhaji ya tura mata ta gani, kallon kuɗin tayi da kyau, tasan idan yayi niya yana bata kuɗi ba ruwansa da tana nata business ɗin, amma kuma wannan na me?, duk da gajiyan da take ji hakan bai hanata miƙewa ta nufi ɗakinsa ba.

Alhaji na kwance yana waya da Amaryansa cikin soyayya, sai Hajiya Sa’adatu ta turo ƙofa ta shigo, kallonta yayi amma bai dai na wayan ba, ita kuwa da mamakin take bin laɓɓansa da kallo dan ta gasƙata abinda kunnenta ke jiyo mata, Alhaji yana murmushi ya ce, “Amaryan Mukhtar a bani aron mintuna biyar kawai, yanzu zan ƙira ki.”

Mami a nata ɓangaren cikin soyayya ta kashe wayan, tana jiransa ya gama abin da yake yi.

Alhaji yana sakar wa Hajiya Sa’adatu murmushi ya ce, “Hajiya ga waje zauna, Uwar gida ran gida daman ina son yin magana da ke, amma naga kina busy, tun da ga ki to bari mu yi maganan yanzu.”

Hajiya Sa’adatu wani irin banzan, malalacin, arnen, ɗan iskan kallo take bin Alhaji da shi, wani irin masifa ne da bala’i ke cin ta, nuna Alhaji ta yi da yatsa rai a ɓace ta ce…

<< Yar Karuwa 18Yar Karuwa 20 >>

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
2
Free daily stories remaining!
×